• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Jihar Ekiti ta gurfanar da wasu mutane 17 da ake zargi da aikata laifuka a jihar tare da kwato wasu makamai a hannunus.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ogundare Dare, ya ce rundunar ta kama mutanen da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

  • Yanzu-yanzu: Tsohon gwamnan Anambra, Mbadinuju Ya Rasu
  • El-Rufai Ya Jinjina Wa Sojoji Kan Kashe Kasurgumin Dan Bindiga, Danwasa A Kaduna

Da ta ke gabatar da wadanda ake zargin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Sunday Abutu, ta ce rundunar ‘yan sandan ta RRS a ranar 6 ga watan Afrilu, ta hanyar kai farmakin daji, sun kama wani Augustine Agboobo, Adeniyi Olamilekan, Williams Ukeuima Friday da Ademoh Gabriel, a cikin dajin da ke kusa da yankin gonakin Igede.

“A yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa cewa su ‘yan kungiyar masu garkuwa da mutane ne da suka gudanar da ayyukan garkuwa da mutane a jihar Ekiti ciki har da sace Ajibade Adeleke a gonar Igede da kuma karbar kudin fansa wasu”.

Abutu ta kara da cewa rundunar ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne tare da hadin gwiwar wasu al’umma a Oke-Ureje da ke Ado-Ekiti a ranar 4 ga watan Afrilu da misalin karfe 22:00 sannan ta kama Saliu Oyebamiji da Ajisefe Mayowa.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Haka kuma, an kama wani fitaccen dan fashi da makami mai suna Jimoh Gani a ranar 4 ga watan Afrilu, bisa laifin yin fashi da makami da yi wa wata dalibar Jami’a fyade a Ikere-Ekiti.

“Lokacin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.”

Rundunar ta kwato kayayyaki daban-daban da suka hada da bindigar gida daya, bindigar maharba guda daya da buhun tabar wiwi da sauransu.

Rundunar ‘yan sandan ta yi kira ga daukacin ‘yan kasar nan da su kula da harkokin tsaro tare da kai rahoton duk wani abu da ya faru a yankinsu ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaFashi Da MakamiLaifukaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasinjoji 12 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ebonyi

Next Post

Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

6 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

6 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

9 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

12 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

14 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

16 hours ago
Next Post
Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.