ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

by Sadiq
3 years ago
APC

Jam’iyyar APC a Jihar Kano ta shigar da kara a gaban kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan Kano da ke zamanta a Miller road, tana kalubalantar nasarar zababben gwamnan Kano, Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar NNPP.

Wakilinmu ya ruwaito cewa an shigar da karar ne a gaban kotun ta hanyar rajista, a ranar 9 ga Afrilu, 2023.

  • Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti
  • NIS Ta Kaddamar Da Shirin ‘Guguwa’ Don Dakile Kwararar ‘Yan Ci-Rani A Ribas

APC ta sanar da kotun cewa sunan zababben gwamnan jihar, Abba Kabiru Yusuf baya cikin jerin rajistar NNPP da ke hannun INEC.

ADVERTISEMENT

APC ta bayyana a cikin karar cewa kafin zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga Maris, 2023, dan takarar jam’iyyar NNPP ya gaza cika sharuddan zama mamba jam’iyyar, don haka ake zargin bai cancanci tsayawa takara a zaben gwamna a karkashin jam’iyyar NNPP ba.

Bugu da kari mai shigar da kara suna rokon kotu da ta rusa wa’adin zaben Abba.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

APC ta bukaci kotun da ta amince da adadin kuri’un da aka kada ba bisa ka’ida ba, don haka a yi la’akari da yadda aka cire adadin kuri’un da aka soke ba bisa ka’ida ba tare da ayyana zaben a matsayin ‘Inconclusive’.

Masu gabatar da kara, sun bukaci NNPP da dan takararta na gwamna da INEC wa’adin kwanaki 21 don amsa batutuwan da masu shigar da kara a kai.

A wani lamari makamancin haka, kotun ta bai wa jam’iyyar APC takardar bukatar duba kayan zaben gwamna, a wani bangare na ci gaba da shari’ar su da NNPP a gaban kotu.

Mai ba da shawara kan harkokin shari’a na jam’iyyar APC Jihar Kano, Abdul Adamu Fagge, ya tabbatar da cewa tawagar jam’iyyar APC ta fara duba kayayyakin zaben da aka yi amfani a kananan hukumomi 44 da ke fadin jihar.

A cewarsa aikin duba kayayyakin yana gudana cikin kwanciyar hankali tare da goyon bayan dukkan bangarorin da abin ya shafa.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa na cewa babu wata tangarda da ake sa ran za ta kawo cikas ga aikin, inda ya ce an ba su damar yin amfani da dukkan kayan ya zuwa yanzu, inda ya ce jam’iyyar za ta bibiyi lamarin har zuwa ga doka.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Xi Jinping: Akwai Makoma Mai Haske A Fannin Raya Sana’o’i Na Musamman A Yankunan Karkara

Xi Jinping: Akwai Makoma Mai Haske A Fannin Raya Sana’o’i Na Musamman A Yankunan Karkara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.