• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Nakiyar Ta Yi Ajalin Sojoji 5 A Borno

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Fashewar Nakiyar Ta Yi Ajalin Sojoji 5 A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sojojin Nijeriya biyar ne suka mutu bayan da motarsu ta taka wata nakiya da ake zargin mayakan jihadi ne suka birne a kusa da kan iyakar Nijar, kamar yadda majiyoyin tsaro suka bayyana.

Rundunar ta kasance cikin sintiri na yau da kullun a kauyen Laayi da ke kusa da garin Damasak a ranar Litinin din da ta gabata lokacin da suka taka wata nakiya, kamar yadda wasu shugabannin mayakan biyu suka shaida wa AFP.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Dirar Mikiya Wurin Taro, Sun Kashe Shugaban Al’umma A Imo 
  • Kotun Sauraron Kararrakin Zabe Ta Fara Zama A Kebbi

Sojojin sun tayar da wasu bama-bamai da ake zargin kungiyar IS da ta kafa daular Islama ta yammacin Afirka (ISWAP) ce ta saka, in ji shugaban mayakan Babakura Kolo.

Fashewar “Ta kashe duka sojojin biyar da ke cikin motar”, in ji shi.

Kolo ya ce mayakan jihadin sun kai hari kauyen ne a daren jiya, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna kauyen hudu da suka hada da shugaban karamar hukumar tare da dasa bama-baman yayin da suke barin kauyen.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Mai magana da yawun sojojin bai amsa kiran da AFP ta yi ba don jin ta bakinsa game da lamarin.

Shugaban ‘yan ta’adda na biyu, Ibrahim Liman, ya bayar da kididdigar adadin wadanda suka mutu.

ISWAP da ta balle daga kungiyar Boko Haram mai da’awar jihadi a shekarar 2016 ta zama babbar barazana a Nijeriya, inda ta kai hari kan sojoji da ke sintiri yayin da suke kashewa tare da yin garkuwa da fasinjoji a shingayen bincike.

Bangarorin biyu masu gaba da juna na masu jihadi sun gwabza fada a cikin ‘yan watannin da suka gabata yayin da sojoji suka zafafa kai hare-hare kan kungiyoyin.

An kafa sojojin ne a manyan sansanoni da aka fi sani a fadin yankin, lamarin da ya bar wasu kauyuka da yankunan karkara ba su da kariya da kuma fuskantar hare-hare.

A watan da ya gabata sojoji uku ne suka mutu sannan wasu hudu suka jikkata tare da wasu fararen hula bakwai a wani fashewar nakiya da ta tashi a kan wata motar soji a wajen garin Banki da ke kusa da kan iyaka da Kamaru.

Rikicin da aka kwashe shekaru 14 ana yi ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 40,000 tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Rikicin dai ya bazu zuwa wasu sassan kasashen Nijar da Chadi da Kamaru da ke makwabtaka da Nijeriya, lamarin da ya sa rundunar hadin gwiwar sojojin yankin ke yaki da mayakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BornoHariISWAPNakiyaSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Atiku Da Obi Suka Fadi Zaben 2023

Next Post

Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10: Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

Related

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

30 minutes ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

1 hour ago
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

4 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

5 hours ago
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya
Labarai

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

6 hours ago
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

8 hours ago
Next Post
Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10:  Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10: Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.