ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Nakiyar Ta Yi Ajalin Sojoji 5 A Borno

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya biyar ne suka mutu bayan da motarsu ta taka wata nakiya da ake zargin mayakan jihadi ne suka birne a kusa da kan iyakar Nijar, kamar yadda majiyoyin tsaro suka bayyana.

Rundunar ta kasance cikin sintiri na yau da kullun a kauyen Laayi da ke kusa da garin Damasak a ranar Litinin din da ta gabata lokacin da suka taka wata nakiya, kamar yadda wasu shugabannin mayakan biyu suka shaida wa AFP.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Dirar Mikiya Wurin Taro, Sun Kashe Shugaban Al’umma A Imo 
  • Kotun Sauraron Kararrakin Zabe Ta Fara Zama A Kebbi

Sojojin sun tayar da wasu bama-bamai da ake zargin kungiyar IS da ta kafa daular Islama ta yammacin Afirka (ISWAP) ce ta saka, in ji shugaban mayakan Babakura Kolo.

ADVERTISEMENT

Fashewar “Ta kashe duka sojojin biyar da ke cikin motar”, in ji shi.

Kolo ya ce mayakan jihadin sun kai hari kauyen ne a daren jiya, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna kauyen hudu da suka hada da shugaban karamar hukumar tare da dasa bama-baman yayin da suke barin kauyen.

LABARAI MASU NASABA

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

Mai magana da yawun sojojin bai amsa kiran da AFP ta yi ba don jin ta bakinsa game da lamarin.

Shugaban ‘yan ta’adda na biyu, Ibrahim Liman, ya bayar da kididdigar adadin wadanda suka mutu.

ISWAP da ta balle daga kungiyar Boko Haram mai da’awar jihadi a shekarar 2016 ta zama babbar barazana a Nijeriya, inda ta kai hari kan sojoji da ke sintiri yayin da suke kashewa tare da yin garkuwa da fasinjoji a shingayen bincike.

Bangarorin biyu masu gaba da juna na masu jihadi sun gwabza fada a cikin ‘yan watannin da suka gabata yayin da sojoji suka zafafa kai hare-hare kan kungiyoyin.

An kafa sojojin ne a manyan sansanoni da aka fi sani a fadin yankin, lamarin da ya bar wasu kauyuka da yankunan karkara ba su da kariya da kuma fuskantar hare-hare.

A watan da ya gabata sojoji uku ne suka mutu sannan wasu hudu suka jikkata tare da wasu fararen hula bakwai a wani fashewar nakiya da ta tashi a kan wata motar soji a wajen garin Banki da ke kusa da kan iyaka da Kamaru.

Rikicin da aka kwashe shekaru 14 ana yi ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 40,000 tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Rikicin dai ya bazu zuwa wasu sassan kasashen Nijar da Chadi da Kamaru da ke makwabtaka da Nijeriya, lamarin da ya sa rundunar hadin gwiwar sojojin yankin ke yaki da mayakan.

MASU ALAKA

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Tsaro

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya
Labarai

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Next Post
Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10:  Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10: Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.