• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa, Ari 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa, Ari 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) ta cafke Barista Hudu Yunusa-Ari, dakataccen kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa a jihar Adamawa (REC) domin fuskantar tuhume-tuhume.

 

A wata sanarwar da ‘yansanda suka fitar a ranar Talata dauke da sanya hannun Kakakin hukumar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya ce, Yunusa-Ari dai ya shiga hannun tawagar ‘yansanda na sashin tsare-tsare, bibiya da sa-ido kan harkokin zabe ne a ranar Talata a Abuja.

  • Majalisar Dokokin Adamawa Ta Tabbatar Da Mace Ta Farko Babban Jojin Jihar

CSP Adejobi ya ce, yanzu haka Hudu yana karkashin kulawar ‘yansanda kuma za su masa tulin tambayoyi dangane da tataburza da kuma dalilan da suka janyo aka gudanar da wasu abubuwan da ba na daidai ba a lokacin kammala zaben gwamnan Jihar Adamawa kwanakin baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Ya ce, “Su ma sauran jami’ai da daidaikun da suke da hannu a lamarin su na nan su na fuskantar tambayoyin jami’an.

 

“Sufeto-janar na ‘yansanda ya bada tabbacin cewa dukkanin wani ko wasu da ke da hannu a lamarin to tabbas za a tuhume shi/su har ma a gurfanar da su kamar yadda yake kunshe a kundin tsarin da doka ya tanadar,” a cewar FPRO.

 

Idan za a tuna dai Ari ya ayyana cewa Sanata Aisha Binani ce ta lashe zaben gwamnan Jihar amma bai bayyana adadin kuri’un da ta lashe zaben a lokacin ba, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce. Daga baya kuma INEC ta ce ba a bi ka’ida ba don haka aka soke wannan tare da ayyana gwamna mai ci a jihar, Ahmadu Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

Kodayake Ari ya fito ya ce shi kam ya nan kan bakarsa domin ya yi amfani da tsarin doka ne wajen ayyana Binani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Next Post

Rundunar ‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar ‘Yan Kasar Hungary A Nijeriya

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

2 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

17 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

19 hours ago
Next Post
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar ‘Yan Kasar Hungary A Nijeriya

Rundunar 'Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar 'Yan Kasar Hungary A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.