ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Ƴansanda

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Kaduna ta cafke mutane shida da ake zargi da aikata garkuwa da mutane, tare da ƙwato makamai daga hannunsu. An samu nasarar ne sakamakon atisayen haɗin gwuiwa da ‘yansanda suka gudanar a sassan jihohin Kaduna da Zamfara.

  • Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

Kakakin Rundunar ‘Yansanda ta Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa cewa lamarin ya samo asali ne daga wani rahoton gaggawa da wani mazaunin Ungwar Ninzom a Jagindi Tasha, ƙaramar hukumar Jama’a ya bayar ranar 22 ga Fabrairu, 2025, inda ya sanar da sace ɗansa, Hussaini Ibrahim, da wasu ‘yan bindiga suka yi.

Bayan samun rahoton, jami’an Ƴansanda daga sashin Kafanchan suka bazama don farautar masu garkuwa da mutanen. Koda yake an ce masu laifin sun tsere a farko, an ceto Hussaini daga dajin da ke kusa da yankin bayan kwana biyu, duk da cewa yana da raunin harbin bindiga a ƙafa. An ba shi kulawa a asibiti sannan aka mayar da shi ga iyalansa.

ADVERTISEMENT

Bincike ya kai ga kama mutane huɗu: Umar Yusuf Jabiri (30), da Buhari Muhammad wanda aka fi sani da “General” (31), da Ahmadu Nasiru (51), da Zakari Saleh (50) — dukkansu mazauna Jagindi Tasha da Gidan Waya. Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga AK-47 guda ɗaya da kuma wasu bindigogi uku ƙirar gida daga hannunsu.

A wani ci gaba kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, rundunar sashin yaƙi da garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin CSP Sani Zuntu, ta gano wani kaya mai ɗauke da bindiga ƙirar AK-47 da aka ɓoye cikin buhu daga Jos, Jihar Filato zuwa Gusau, Jihar Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Hakan ya haifar da cafke Abdulmumin Sani da Naziru Musa a Gusau, inda ake zargin sun je karɓar bindigar. Rundunar ta ce za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike. Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da ƙwazon jami’an da suka gudanar da waɗannan atisayen tare da tabbatar wa da jama’a cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen kawar da ‘yan ta’adda daga jihar.

Ƴansanda
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
  • Abubakar Sulaiman
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.