• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Nadin Sarautar Sarki Charles A Landan

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Zai Halarci Nadin Sarautar Sarki Charles A Landan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bi sahun sauran shugabannin kasashen duniya domin nadin sarautar Charles III da uwargidansa Camilla a matsayin mai martaba sarki da Sarauniyar Ingila.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba.

  • Saboda Ziyarar Tinubu, Wike Ya Ba Da Hutu, Ya Umarci Rufe Kasuwanni
  • Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

Adesina ya ce shugaban kasar zai tafi birnin Landan na Birtaniya a ranar Laraba domin bikin nadin sarautar da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 6 ga watan Mayu.

“Kafin nadin sarautar, sakatariyar Commonwealth za ta yi amfani da damar taron shugabannin da za a yi a Landan don karbar bakuncin taron koli na shugabannin gwamnatocin kasashen Commonwealth a ranar Juma’a 5 ga Mayu.

Sanarwar ta kara da cewa “An bukaci shugaba Buhari da ya halarci taron da za a tattauna kan makomar kasashen Commonwealth da kuma rawar da matasa za su taka.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Kebbi Ya NaÉ—a Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin KuÉ—in Fansho

Shugaban zai samu rakiyar sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama; Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed; mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Manjo-Janar Babagana Monguno (mai ritaya); Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ambasada Ahmed Abubakar; Shugabar hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa; da sauran manyan jami’an gwamnati.

A watan Nuwamba ne Buhari ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham domin kulla alaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya.

Shugaban kasar ya ce sarkin na yanzu, wanda aka nada sarauta bayan rasuwar mahaifiyarsa, “yana magana da Nijeriya sosai kuma yana son dangantakarsu ta ci gaba.”

Nijeriya, wacce a da ta kasance kasar da Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka, ta samu ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, 1960 a lokacin mulkin Sarauniya Elizabeth ta biyu wadda ta rasu a watan Satumban 2022 tana da shekaru 96.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariIngilaLandanNadin SarautaSarauniya ElizabethSarki Charles III
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saboda Ziyarar Tinubu, Wike Ya Ba Da Hutu, Ya Umarci Rufe Kasuwanni

Next Post

Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku

Related

Gwamnan Kebbi Ya NaÉ—a Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 
Manyan Labarai

Gwamnan Kebbi Ya NaÉ—a Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

5 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin KuÉ—in Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin KuÉ—in Fansho

6 hours ago
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

8 hours ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

9 hours ago
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

11 hours ago
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

15 hours ago
Next Post
Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku

Sakon Buhari Ga 'Yan Jarida: Na Kare 'Yancinku

LABARAI MASU NASABA

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da KarÉ“ar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da KarÉ“ar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

August 28, 2025
Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa

Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa

August 28, 2025
Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

August 28, 2025
An Bude Bikin Nune-Nune Na Masana’antar Manyan Bayanai Ta Big Data A Kudu Maso Yammacin Sin

An Bude Bikin Nune-Nune Na Masana’antar Manyan Bayanai Ta Big Data A Kudu Maso Yammacin Sin

August 28, 2025
AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

August 28, 2025
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Shigo Da Su Daga Kasashe Masu Karancin Ci Gaba Na Afrika Ya Karu Da Kaso 10.2 Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Shigo Da Su Daga Kasashe Masu Karancin Ci Gaba Na Afrika Ya Karu Da Kaso 10.2 Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

August 28, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

August 28, 2025
Shugabannin Kasashe 26 Za Su Halarci Bikin Ranar Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa A Ran 3 Ga Satumba

Shugabannin Kasashe 26 Za Su Halarci Bikin Ranar Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa A Ran 3 Ga Satumba

August 28, 2025
Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

August 28, 2025
Jimillar Kudaden Jigilar Kayayyaki a Watanni 7 Na Farkon Bana a Sin Ta Zarce Rmb Yuan Tiriliyan 200

Jimillar Kudaden Jigilar Kayayyaki a Watanni 7 Na Farkon Bana a Sin Ta Zarce Rmb Yuan Tiriliyan 200

August 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.