ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Nadin Sarautar Sarki Charles A Landan

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bi sahun sauran shugabannin kasashen duniya domin nadin sarautar Charles III da uwargidansa Camilla a matsayin mai martaba sarki da Sarauniyar Ingila.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba.

  • Saboda Ziyarar Tinubu, Wike Ya Ba Da Hutu, Ya Umarci Rufe Kasuwanni
  • Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

Adesina ya ce shugaban kasar zai tafi birnin Landan na Birtaniya a ranar Laraba domin bikin nadin sarautar da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 6 ga watan Mayu.

ADVERTISEMENT

“Kafin nadin sarautar, sakatariyar Commonwealth za ta yi amfani da damar taron shugabannin da za a yi a Landan don karbar bakuncin taron koli na shugabannin gwamnatocin kasashen Commonwealth a ranar Juma’a 5 ga Mayu.

Sanarwar ta kara da cewa “An bukaci shugaba Buhari da ya halarci taron da za a tattauna kan makomar kasashen Commonwealth da kuma rawar da matasa za su taka.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Shugaban zai samu rakiyar sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama; Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed; mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Manjo-Janar Babagana Monguno (mai ritaya); Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ambasada Ahmed Abubakar; Shugabar hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa; da sauran manyan jami’an gwamnati.

A watan Nuwamba ne Buhari ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham domin kulla alaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya.

Shugaban kasar ya ce sarkin na yanzu, wanda aka nada sarauta bayan rasuwar mahaifiyarsa, “yana magana da Nijeriya sosai kuma yana son dangantakarsu ta ci gaba.”

Nijeriya, wacce a da ta kasance kasar da Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka, ta samu ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, 1960 a lokacin mulkin Sarauniya Elizabeth ta biyu wadda ta rasu a watan Satumban 2022 tana da shekaru 96.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku

Sakon Buhari Ga 'Yan Jarida: Na Kare 'Yancinku

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.