ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Nadin Sarautar Sarki Charles A Landan

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bi sahun sauran shugabannin kasashen duniya domin nadin sarautar Charles III da uwargidansa Camilla a matsayin mai martaba sarki da Sarauniyar Ingila.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba.

  • Saboda Ziyarar Tinubu, Wike Ya Ba Da Hutu, Ya Umarci Rufe Kasuwanni
  • Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

Adesina ya ce shugaban kasar zai tafi birnin Landan na Birtaniya a ranar Laraba domin bikin nadin sarautar da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 6 ga watan Mayu.

ADVERTISEMENT

“Kafin nadin sarautar, sakatariyar Commonwealth za ta yi amfani da damar taron shugabannin da za a yi a Landan don karbar bakuncin taron koli na shugabannin gwamnatocin kasashen Commonwealth a ranar Juma’a 5 ga Mayu.

Sanarwar ta kara da cewa “An bukaci shugaba Buhari da ya halarci taron da za a tattauna kan makomar kasashen Commonwealth da kuma rawar da matasa za su taka.”

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Shugaban zai samu rakiyar sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama; Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed; mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Manjo-Janar Babagana Monguno (mai ritaya); Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ambasada Ahmed Abubakar; Shugabar hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa; da sauran manyan jami’an gwamnati.

A watan Nuwamba ne Buhari ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham domin kulla alaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya.

Shugaban kasar ya ce sarkin na yanzu, wanda aka nada sarauta bayan rasuwar mahaifiyarsa, “yana magana da Nijeriya sosai kuma yana son dangantakarsu ta ci gaba.”

Nijeriya, wacce a da ta kasance kasar da Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka, ta samu ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, 1960 a lokacin mulkin Sarauniya Elizabeth ta biyu wadda ta rasu a watan Satumban 2022 tana da shekaru 96.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku

Sakon Buhari Ga 'Yan Jarida: Na Kare 'Yancinku

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.