ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Nadin Sarautar Sarki Charles A Landan

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bi sahun sauran shugabannin kasashen duniya domin nadin sarautar Charles III da uwargidansa Camilla a matsayin mai martaba sarki da Sarauniyar Ingila.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba.

  • Saboda Ziyarar Tinubu, Wike Ya Ba Da Hutu, Ya Umarci Rufe Kasuwanni
  • Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

Adesina ya ce shugaban kasar zai tafi birnin Landan na Birtaniya a ranar Laraba domin bikin nadin sarautar da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 6 ga watan Mayu.

ADVERTISEMENT

“Kafin nadin sarautar, sakatariyar Commonwealth za ta yi amfani da damar taron shugabannin da za a yi a Landan don karbar bakuncin taron koli na shugabannin gwamnatocin kasashen Commonwealth a ranar Juma’a 5 ga Mayu.

Sanarwar ta kara da cewa “An bukaci shugaba Buhari da ya halarci taron da za a tattauna kan makomar kasashen Commonwealth da kuma rawar da matasa za su taka.”

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Shugaban zai samu rakiyar sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama; Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed; mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Manjo-Janar Babagana Monguno (mai ritaya); Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ambasada Ahmed Abubakar; Shugabar hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa; da sauran manyan jami’an gwamnati.

A watan Nuwamba ne Buhari ya gana da Sarki Charles III a fadar Buckingham domin kulla alaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya.

Shugaban kasar ya ce sarkin na yanzu, wanda aka nada sarauta bayan rasuwar mahaifiyarsa, “yana magana da Nijeriya sosai kuma yana son dangantakarsu ta ci gaba.”

Nijeriya, wacce a da ta kasance kasar da Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka, ta samu ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, 1960 a lokacin mulkin Sarauniya Elizabeth ta biyu wadda ta rasu a watan Satumban 2022 tana da shekaru 96.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Sakon Buhari Ga ‘Yan Jarida: Na Kare ‘Yancinku

Sakon Buhari Ga 'Yan Jarida: Na Kare 'Yancinku

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.