ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Burtaniya

Dan takarar shugaban kasa a karkashin lemar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya fito ya yi bayanin hakikanin abubuwan da suka wakana a tsakaninsu da jami’an hukumar kula da shige da fice a filin sauka da tashin jiragen na kasa da kasa da ke Heathrow a kasar Landan sa’ilin tafiyar da ya yi don bikin Ista. 

 

A hirarsa da Arise News Channel ranar Talata da wakilinmu ya saurara, tsohon gwamnan Jihar Anambra ya fayyace abin da ya fahimta, inda ya ce, jami’an Gwamnatin Burtaniya ba su taba cafke shi balle su tsare shi ba.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Belin Peter Obi Daga Hannun Birtaniya

Ya ce, abun da ya faru a filin Jirgin Heathrow, wani shigen binciken Immigration ne yayin da ya mika musu shaidarsa domin tantancewa sai suka yi zargin cewa an kwafi shaidarsa ko ironsa guda biyu ne don haka suka bibiyi bayanansa da gano cewa an kwafi irin nasa ne.

 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Obi ya ce, dan tsayar da shi na ‘yan mintina kawai aka yi sabanin bayanan da jam’iyyarsa ta fitar na cewa an dauki tsawon lokaci ana masa tukin tambayoyi.

 

Ya ce: “Sam kwata-kwata ba a kamani ba, ba a tsare ni ba. Sannan, ban aikata kowani irin laifi ba. An tsayar da ni a wurin binciken da aka saba na yau da kullum na hukumar kula da shige da fice saboda bayanan shaidata ya nuna shaida har biyu, kuma dududu bai wuce mintina 20 aka kammala komai.

 

“Ina rayuwa a Burtaniya tun 1993 har zuwa 2005. Daga wancan lokacin zuwa yanzu shekaru 30 kenan. Ba a taba zaunar da ni aka min tuhuma, kamawa ko tsarewa a kowace kasa a fadin duniyar nan. Ban tana samun kaina a bisa wani dalili da aka tuhumeni kan aikata wani laifi ba.

 

“A zahirin gaskiya, shigen binciken ne na yau da kullum, kuma jami’an sun bani dukkanin wata girmamawa sa’ilin da suke min tambayoyi, har ma suka shaida min cewa an kwafi shaidata don haka na kiyaye,” ya shaida.

 

Obi ya kara da cewa duk da yana da cikakken izirin zama a UK, amma ya zabi ya dawo Nijeriya, ya kara da cewa, “Ni haifafen dan Nijeriya ne. Ina kuma son na yi rayuwata a nan na mutu a nan gida Nijeriya”.

 

Ya ce, yana da rubutaccce bayani daga Gwamnatin Burtaniya da ke fayyace cewa ba tsare shi aka yi ba, illa iyaka an tsayar da shi a wurin binciken hukumar shige da fice domin duba bayanan shaidar shige da ficensa na ‘yan mintina kalilan.

Burtaniya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.