• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birnin Legas Ya Zama Na Biyu Mafi Muni Wajen Yin Rayuwa A Duniya

by Sadiq
3 years ago

Kungiyar harkokin kasuwanci ta duniya, (EIU), ta bayyana birnin Legas, wanda ya ke babban birnin kasuwanci a Nijeriya, a matsayin birni na biyu mafi munin gudanar da rayuwa a duniya.

EIU ta sanya Legas a matsayi na 171 daga cikin kasashe 172 a cikin jerin biranen da za a iya rayuwa a duniya, a kashin farko na shekarar 2022, bayan sabbin alkaluma da ta fitar.

  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Da Zai Ke Sanya Ido A Shafukan TikTok Da Instagram
  • Ra’ayoyinku A Kan Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa Na APC Na Wucin-Gadi

Wannan rahoto ya sanya birni mafi kyawu a Najeriya ya zama mafi muni a Afirka yayin da Damascus (Syria) da Tripoli (Libya) ke bin sahun tare da Legas (Najeriya), wanda suke fuskantar tashin hankali na zamantakewa, ta’addanci da rikice-rikice.

“Biranen mafi munin rayuwa su ne Damascus a Siriya, Legas a Najeriya, Tripoli a Libya, Algiers a Aljeriya da Karachi a Pakistan, wadanda suka samu maki 30.7, 32.2, 34.2, 37.0 da 37.5.

“EIU ta kara bayyana manyan biranen duniya guda biyar da suka fi dadin rayuwa a duniya wadanda suka hada da Vienna, Ostiriya wanda ya samu maki 99. 1; Copenhagen, Denmark sun samu 98.0; Zurich, Switzerland na da maki 96.3; Calgary, Kanada na da 96.3, Vancouver 96.1.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

“Duk da haka, yawancin biranen da ke cikin kasa goma sun inganta kimarsu idan aka kwatanta da bara, kamar yadda cutar ta COVID-19 ta haifar da matsin lamba,” in ji EIU.

 

EIU, ta sanya birane 173 a duniya kan abubuwa daban-daban, ciki har da kiwon lafiya, yawan laifuka, kwanciyar hankali, siyasa da kayayyakin more rayuwa d.

EIU na nazarin ingancin kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, kwanciyar hankali, da al’adu lokacin da ake tantance yanayin rayuwa na kowane birni.

Fiye da abubuwa 30 aka yi la’akari da su yayin kididdigar kowane matsayi, wanda sai aka hada su zuwa ma’aunin nauyi tsakanin daya zuwa 100.

Daga alamomin da aka yi amfani da su wajen kididdigar sun hada kwanciyar hankali, kiwon lafiya, al’adu, muhalli, ilimi da ababen more rayuwa, Legas ta samu maki 20.0, 20.8, 44.9, 25.0 da 46.4, wanda yasa ta samu maki 32.2 daga jimillar maki 100.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Next Post
Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.