• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa Na APC Na Wucin-Gadi

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Siyasa
0
Ra’ayoyinku A Kan Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa Na APC Na Wucin-Gadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barkanmu da saduwa a wannan fili na Ra’ayi Riga, wannan mako mun kawo muku ra’ayin masu bibiyarmu ne a kan sabon salo na dan takarar Mataimakin Shugaban Kasa na ‘Wucin-gadi’ da Jami’yyar APC ta tura wa INEC.

Shamsuddeen Ahmad Idris
Ai daman da kai da kaya duk mallakan wuya ne, wannan ba wani abu ba ne, ai kasarma tasu ce, don haka yadda suka ga dama za su yi.

  • Ina Jin Takaici Da Damuwa Kan Yadda Ake Fita Daga Jam’iyyarmu Ta APC —Abdullahi Adamu

Sani Bello Kano
Ni ban san ma me zan ce ba matsala dai an sameta kasa ta gama rasa jagoranci duk wanda za su kawo sai an ji ya yi wata katobara kuma babu dama talaka ya yi magana basa jin ko wane yare sai zancen kudi
Sannan kuma hakan ya nuna basu ma shirya wa kasar komai ba sai son ransu babu wani tanadin alkhairi, kawai mu dai babu abinda ya kamace mu sai addu’ar Allah ya zaba mana mafi alkhairi

It’z Sam Dambatta
Ai wannan shi yake nuna mana cewa kawai mulkin ake so ayi. Bawai kawo wa kasa mafita ba, mu dai fatan mu Allah ya zaba mana mafi alkhairi

Umar Ibrahim Umar
Allah ya kyauta, wani abu sai Nijeriya wannan shi yake nuna maka cewa tun daga tsarin tsayawa takara babu tsari babu shiri ba a tsara wanda zai yi mataimakin wanda zai yi mataimakin dan takara ba har yanzu, kenan yana nuna koda ace nasara aka yi babu wani shiri kenan a kasa don gudanar da shugabanci nagari, Allah dai Ya taimaka mana, Amin

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Omar Naseer Imam
Toh abin dai kam ya zo mana da mamaki, fatanmu shi ne Allah ya bamu shugabanni nagari

Sulaiman Muhammad
To wannan sai lauyoyi

Bashir Ibrahim Matazu
Shi wannan tsarin na aan takarar Mataimaki na wucin-gadi shi ne ke nuna maka cewa ita kanta kasar basu shirya mata komai ba sai dai kawai Allah Ya bamu mafita.

Ibrahim Hassan Baban Adila
Anya wannan jam’iyyar APC ba shiga cikin rudani ba kuwa?, tayaya aka taba yin haka, wannan ya nuna wa mutane suna jin shakkan jam’iyyar PDP kenan kuma sun rasa mafita. Daga karshe Allah ya zaba mana shuwagabanni nagari kuma mafi alkhairi a garemu, Ameen. Ibrahim Hassan Minister Baban Adila da Ansar, Gombe

Rchp Ahmad Shehu Babaldu
Nijeriya kasarmu ta gado!
Yanzu inda ace kasa ce mai doka, kamata ya yi ace wadda suka dauki mataimaka na wucin gadi a hukuntasu daidai da abinda suka aikata tunda sun sabawa dokar zabe ta kasa. Amma abin takaici sai gashi jam’iyya mai mulki ce ta fara fito da wannan salo da ya ci karo da dokar INEC.
Allah dai muke roko da ya zaba mana shugabanni nagari ba don halinmu ba, don Sayyidina Rasulullah sallallahu alaihi wa sallam.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Toh wannan abu sai dai muce Allah ya kaimu lokachin mugani na tabbar da cewa babu wannan doka duba da yadda jam’iyya mai mulki ce ta nemi hakan da dai jam’iyyar adawa ce ta nemi hakan sai mu yadda da wannan magana da hukumar zabe ta kasa INEC ta yi mu dai fatammu dai akoda yaushe shi ne Allah [S.W.T] ya zaba mana shugabanni nagari masu tausayin al’umma.

Abban Goba
Duk wasu kulle-kulle da za a yi a kowace jam’iyya indai ba alkhairi ba ne Allah ya kifar, ya yi mana zabi na alkhairi

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya wannan salon da APC ta dauko hakan ya nuna cewa akwai luje cikin nadi domin in da sun shirya yin gaskiya to yakamata su bayyana wa mutane gaskiyar wanda zai zama mataimaki, mu dai fatan mu Allah duk wanda zai zama cikas ga kasarmu Allah karka bashi. Allah ya baiwa wanda yake tausayin mu Allah ya zaba mana mafi alkairi ko daga wanne yanki yake

Sadeek Rufa’i Ɗanguguwa
Nijeriya Jaga-jaga, inji wani tsohon wamaki, bashakka wannan batun ya alamta mana cewar shugabancin wannan kasa sam-sam basu shirya wa mulkin wannan kasa ba ko kadan. Sai fatan Allah ya kawo mana mafita ta alkairi.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Badi ba rai kenan, a Nijeriya ne kullum da sabon abinda zai bullo, yau za ka ji shugaba wane ya ce abu kaza, gobe kuma za ka ji wani ya fito da na shi daban.
Amma ni a fahimtana tunda har ki ka ga wancen batun na mataimakin shugaban kasa ya zo a wannan salon, to lallai akwai yiyuwar salon zai taka rawa a siyasance. Allah dai ya zaba mana shugabanni na gari.

Justice Mudansir
Atiku abubakar ya burgeni kuma wannan alamu ne na nasararsa, Alhaji Atiku Abubakar a shekarar 2023, dalilina kuwa shi ne, yakamata a samu barakar neman murdiya ta bangaren PDP, amma sai gashi a Jam’iyya maici ta APC ake kokarin aikata aikin da ya sabawa dokar hukumar zabe ta kasa wato INEC idan har kuma shugaban nata ya amince to zamu ce sayansa jam’iyyar APC ta yi

Sani Ladan
Wannan abin mamaki da yawa yake, to amma mudai masu sauraro ne hakika zan so ace naga karshen wannan shirin da jam’iyyata take yi domin zamu iya kiran ta sabuwar dabarar siyasa a kasata, INEC da APC muna jira muga yadda za ta kaya.

Muhd Basheer Sa’ad
Wannan ai alama ce ta cewar wannan jam’iya son ran ta kawai take yi, kuma tana takama ne da cewar gwamnati a hannun ta take. Kuma hakan raina dimokaradiyya ne tunda dai babu hakan a cikin kudin tsarin dokar zaben kasar.

Yusuf Muhammad Jalingo
Mudai mun san babu wannan acikin doka kamar yadda INEC ta fada amma zamu jira mu ji in tusa zai hura wuta

Muhd Basheer Sa’ad
Wannan ai alama ce ta cewar, wannan jam’iyyar son ran ta kawai take, kuma tana takama ne da cewar gwamnati a hannun ta take.
Kuma hakan raina Demokaradiyya ne tunda dai babu hakan a cikin kudin tsarin dokar za6en kasar.

Yusuf Muhammad Jalingo
Mudai mun san babu wannan a cikin doka kamar yadda INEC ta fada amma zamu jira muji in tusa zai hura wutaaisha


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Aka Gama Rarraba Wa Deliget Kudi, Sai Kuma Me? (Ra’ayinmu)

Next Post

INEC Ta Kara Yawan Na’urorin Rajistar Katin Zabe A Jihar Katsina

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

3 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

11 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

14 hours ago
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

2 days ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

2 days ago
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
Siyasa

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

2 days ago
Next Post
INEC Ta Kara Yawan Na’urorin Rajistar Katin Zabe A Jihar Katsina

INEC Ta Kara Yawan Na’urorin Rajistar Katin Zabe A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.