ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa Na APC Na Wucin-Gadi

by Aisha Seyoji
4 years ago
APC

Barkanmu da saduwa a wannan fili na Ra’ayi Riga, wannan mako mun kawo muku ra’ayin masu bibiyarmu ne a kan sabon salo na dan takarar Mataimakin Shugaban Kasa na ‘Wucin-gadi’ da Jami’yyar APC ta tura wa INEC.

Shamsuddeen Ahmad Idris
Ai daman da kai da kaya duk mallakan wuya ne, wannan ba wani abu ba ne, ai kasarma tasu ce, don haka yadda suka ga dama za su yi.

  • Ina Jin Takaici Da Damuwa Kan Yadda Ake Fita Daga Jam’iyyarmu Ta APC —Abdullahi Adamu

Sani Bello Kano
Ni ban san ma me zan ce ba matsala dai an sameta kasa ta gama rasa jagoranci duk wanda za su kawo sai an ji ya yi wata katobara kuma babu dama talaka ya yi magana basa jin ko wane yare sai zancen kudi
Sannan kuma hakan ya nuna basu ma shirya wa kasar komai ba sai son ransu babu wani tanadin alkhairi, kawai mu dai babu abinda ya kamace mu sai addu’ar Allah ya zaba mana mafi alkhairi

ADVERTISEMENT

It’z Sam Dambatta
Ai wannan shi yake nuna mana cewa kawai mulkin ake so ayi. Bawai kawo wa kasa mafita ba, mu dai fatan mu Allah ya zaba mana mafi alkhairi

Umar Ibrahim Umar
Allah ya kyauta, wani abu sai Nijeriya wannan shi yake nuna maka cewa tun daga tsarin tsayawa takara babu tsari babu shiri ba a tsara wanda zai yi mataimakin wanda zai yi mataimakin dan takara ba har yanzu, kenan yana nuna koda ace nasara aka yi babu wani shiri kenan a kasa don gudanar da shugabanci nagari, Allah dai Ya taimaka mana, Amin

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Omar Naseer Imam
Toh abin dai kam ya zo mana da mamaki, fatanmu shi ne Allah ya bamu shugabanni nagari

Sulaiman Muhammad
To wannan sai lauyoyi

Bashir Ibrahim Matazu
Shi wannan tsarin na aan takarar Mataimaki na wucin-gadi shi ne ke nuna maka cewa ita kanta kasar basu shirya mata komai ba sai dai kawai Allah Ya bamu mafita.

Ibrahim Hassan Baban Adila
Anya wannan jam’iyyar APC ba shiga cikin rudani ba kuwa?, tayaya aka taba yin haka, wannan ya nuna wa mutane suna jin shakkan jam’iyyar PDP kenan kuma sun rasa mafita. Daga karshe Allah ya zaba mana shuwagabanni nagari kuma mafi alkhairi a garemu, Ameen. Ibrahim Hassan Minister Baban Adila da Ansar, Gombe

Rchp Ahmad Shehu Babaldu
Nijeriya kasarmu ta gado!
Yanzu inda ace kasa ce mai doka, kamata ya yi ace wadda suka dauki mataimaka na wucin gadi a hukuntasu daidai da abinda suka aikata tunda sun sabawa dokar zabe ta kasa. Amma abin takaici sai gashi jam’iyya mai mulki ce ta fara fito da wannan salo da ya ci karo da dokar INEC.
Allah dai muke roko da ya zaba mana shugabanni nagari ba don halinmu ba, don Sayyidina Rasulullah sallallahu alaihi wa sallam.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Toh wannan abu sai dai muce Allah ya kaimu lokachin mugani na tabbar da cewa babu wannan doka duba da yadda jam’iyya mai mulki ce ta nemi hakan da dai jam’iyyar adawa ce ta nemi hakan sai mu yadda da wannan magana da hukumar zabe ta kasa INEC ta yi mu dai fatammu dai akoda yaushe shi ne Allah [S.W.T] ya zaba mana shugabanni nagari masu tausayin al’umma.

Abban Goba
Duk wasu kulle-kulle da za a yi a kowace jam’iyya indai ba alkhairi ba ne Allah ya kifar, ya yi mana zabi na alkhairi

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya wannan salon da APC ta dauko hakan ya nuna cewa akwai luje cikin nadi domin in da sun shirya yin gaskiya to yakamata su bayyana wa mutane gaskiyar wanda zai zama mataimaki, mu dai fatan mu Allah duk wanda zai zama cikas ga kasarmu Allah karka bashi. Allah ya baiwa wanda yake tausayin mu Allah ya zaba mana mafi alkairi ko daga wanne yanki yake

Sadeek Rufa’i Ɗanguguwa
Nijeriya Jaga-jaga, inji wani tsohon wamaki, bashakka wannan batun ya alamta mana cewar shugabancin wannan kasa sam-sam basu shirya wa mulkin wannan kasa ba ko kadan. Sai fatan Allah ya kawo mana mafita ta alkairi.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Badi ba rai kenan, a Nijeriya ne kullum da sabon abinda zai bullo, yau za ka ji shugaba wane ya ce abu kaza, gobe kuma za ka ji wani ya fito da na shi daban.
Amma ni a fahimtana tunda har ki ka ga wancen batun na mataimakin shugaban kasa ya zo a wannan salon, to lallai akwai yiyuwar salon zai taka rawa a siyasance. Allah dai ya zaba mana shugabanni na gari.

Justice Mudansir
Atiku abubakar ya burgeni kuma wannan alamu ne na nasararsa, Alhaji Atiku Abubakar a shekarar 2023, dalilina kuwa shi ne, yakamata a samu barakar neman murdiya ta bangaren PDP, amma sai gashi a Jam’iyya maici ta APC ake kokarin aikata aikin da ya sabawa dokar hukumar zabe ta kasa wato INEC idan har kuma shugaban nata ya amince to zamu ce sayansa jam’iyyar APC ta yi

Sani Ladan
Wannan abin mamaki da yawa yake, to amma mudai masu sauraro ne hakika zan so ace naga karshen wannan shirin da jam’iyyata take yi domin zamu iya kiran ta sabuwar dabarar siyasa a kasata, INEC da APC muna jira muga yadda za ta kaya.

Muhd Basheer Sa’ad
Wannan ai alama ce ta cewar wannan jam’iya son ran ta kawai take yi, kuma tana takama ne da cewar gwamnati a hannun ta take. Kuma hakan raina dimokaradiyya ne tunda dai babu hakan a cikin kudin tsarin dokar zaben kasar.

Yusuf Muhammad Jalingo
Mudai mun san babu wannan acikin doka kamar yadda INEC ta fada amma zamu jira mu ji in tusa zai hura wuta

Muhd Basheer Sa’ad
Wannan ai alama ce ta cewar, wannan jam’iyyar son ran ta kawai take, kuma tana takama ne da cewar gwamnati a hannun ta take.
Kuma hakan raina Demokaradiyya ne tunda dai babu hakan a cikin kudin tsarin dokar za6en kasar.

Yusuf Muhammad Jalingo
Mudai mun san babu wannan a cikin doka kamar yadda INEC ta fada amma zamu jira muji in tusa zai hura wutaaisha

APC
Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
INEC Ta Kara Yawan Na’urorin Rajistar Katin Zabe A Jihar Katsina

INEC Ta Kara Yawan Na’urorin Rajistar Katin Zabe A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.