ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birnin Legas Ya Zama Na Biyu Mafi Muni Wajen Yin Rayuwa A Duniya

by Sadiq
4 years ago

Kungiyar harkokin kasuwanci ta duniya, (EIU), ta bayyana birnin Legas, wanda ya ke babban birnin kasuwanci a Nijeriya, a matsayin birni na biyu mafi munin gudanar da rayuwa a duniya.

EIU ta sanya Legas a matsayi na 171 daga cikin kasashe 172 a cikin jerin biranen da za a iya rayuwa a duniya, a kashin farko na shekarar 2022, bayan sabbin alkaluma da ta fitar.

  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Da Zai Ke Sanya Ido A Shafukan TikTok Da Instagram
  • Ra’ayoyinku A Kan Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa Na APC Na Wucin-Gadi

Wannan rahoto ya sanya birni mafi kyawu a Najeriya ya zama mafi muni a Afirka yayin da Damascus (Syria) da Tripoli (Libya) ke bin sahun tare da Legas (Najeriya), wanda suke fuskantar tashin hankali na zamantakewa, ta’addanci da rikice-rikice.

ADVERTISEMENT

“Biranen mafi munin rayuwa su ne Damascus a Siriya, Legas a Najeriya, Tripoli a Libya, Algiers a Aljeriya da Karachi a Pakistan, wadanda suka samu maki 30.7, 32.2, 34.2, 37.0 da 37.5.

“EIU ta kara bayyana manyan biranen duniya guda biyar da suka fi dadin rayuwa a duniya wadanda suka hada da Vienna, Ostiriya wanda ya samu maki 99. 1; Copenhagen, Denmark sun samu 98.0; Zurich, Switzerland na da maki 96.3; Calgary, Kanada na da 96.3, Vancouver 96.1.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Duk da haka, yawancin biranen da ke cikin kasa goma sun inganta kimarsu idan aka kwatanta da bara, kamar yadda cutar ta COVID-19 ta haifar da matsin lamba,” in ji EIU.

 

EIU, ta sanya birane 173 a duniya kan abubuwa daban-daban, ciki har da kiwon lafiya, yawan laifuka, kwanciyar hankali, siyasa da kayayyakin more rayuwa d.

EIU na nazarin ingancin kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, kwanciyar hankali, da al’adu lokacin da ake tantance yanayin rayuwa na kowane birni.

Fiye da abubuwa 30 aka yi la’akari da su yayin kididdigar kowane matsayi, wanda sai aka hada su zuwa ma’aunin nauyi tsakanin daya zuwa 100.

Daga alamomin da aka yi amfani da su wajen kididdigar sun hada kwanciyar hankali, kiwon lafiya, al’adu, muhalli, ilimi da ababen more rayuwa, Legas ta samu maki 20.0, 20.8, 44.9, 25.0 da 46.4, wanda yasa ta samu maki 32.2 daga jimillar maki 100.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.