• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

A daidai lokacin da gwamnatin Muhammadu Buhari ke shirye-shirye mika mulki ga sabuwar gwamnati ma’aikata musamman masu rike da mukaman siyasa suna fuskantar rasa ayyukansu saboda sabbin nade-naden da za a yi a sabuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, kamar dai yadda binciken da LEADERSHIP HAUSA ta yi.

Duk da yake lamarin rasa aiki ba wani sabon abu ba ne, musamman ganin gwamnati mai kamawa za ta nada mutanen ta ne da za su yi aiki tare, amma fargarbar da ke tattare da rasa aiki ya kara kamari a tsakanin masu rike da mukaman siyasa a wannan lokacin.

  • Wasu Ke Neman Bata Mana Suna Kan Rikicin Shugabancin APGA – INEC
  • Gwamnati Ta Amince Da Sabbin Manufofin Bunkasa Samar Da Motoci A Nijeriya 

Binciken mu ya nuna cewa, rasa ayyukan zai dangantaka ne da irin tsare-tsaren da yadda sabuwar gwamnatin ta shirya gudanarwa da ayukan da za ta sa a gaba da zaran an rantsar da ita.

A baya, wasu sabbin gwamnatin da aka yi su kan zabi kawar da kowa ne da ya yi aiki da gwamnati mai barin gado wanda hakan ke haifar da rashin ayyukan yi mai dimbin yawa yayin da wasu gamnatin ke zabar samar da canjji a sannu da hankali har a kai ga canza wadanda suka yi wa tsohuwar gwamnati aiki a samar da sabbin mutane da za su yi aiki da sabuwar gwamnatin gaba daya.

Lamarin a wannan lokacin ya za da sabon salo musamman ganin kasar na fuskantar matsalolin tattalin arziki, abin da ya sa ake ganin gwamnatin na Bola Tinubu za ta nemai aiwatar da rahoton kwamitjn nan na Stebe Oronsaye wanda ya bayar da shawarar sake fasalin ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya, akalla kwamitin ya nemi a hada wasu ma’aikatu a wuri daya ko kuma a rusa wasu ma’aikatan ba tare da wata lokaci ba, wannan aiki kuma ana ganin zai shafi akalla ma’aikata fiye 102 yayin da kuma za a umarci wasu ma’aikatan su fuskanci nema wa kansu kudaden shiga.

Nijeriya na ci gaba da farfadowa daga rikicin karayar tattalin arziki da aka fuskanta a tsakanin shekarar 2016 zuwa 2017, da matsalar da cutar korona ya haifar a shekarar 2020 wadanda suka tagayyara tsarin tattalin arzikin kasa.

Yayin da gwanmati ke kokarin ganijn ta sauke nauyin da ke a kanta na biyan albashi da sauransu, ta kuma tilastawa kanta karbar basuka don gudanar da manyan ayyuka akwai manyan fargaban cewa nauyi zai yi wa gwamnati mai kamawa yawa ta yadda ba za ta iya biyan hakokin da ke a kan ta ba na al’umma Nijeriya kamar yadda ta yi alkawari.

In har gwfamnati mai kamawa ta bata yanke shawarar rage ma’akatun gwamnati, hakan zai kai ga rasa ayyukan yi a tsakanijn ‘yan Nijeriya, abin kuma da zai fi shafar masu mukaman siyasa saboda ana ganin su a matsayin cima zaune.

Amma kuma ga dukkan masu mukaman siyasa ne za a iya kira da cima zaune ba, musamman ganin ana iya amfani da su wajen tabbatar da ayyukan gwamnati na cigaba daga gwamnatin da ke barin gado zuwa gwamnatin mai kamawa.

Abin kura kuma ba wai rasa aikin zai tsaya ne kawai a ikajn masu rike da mukaman siyasa kawai ba ne, lamarin zai iya sahafar wasu ma’aikatun gwamnati da ke fiuskantar matsalar rashin kudaden gudanarwa.

A wannan karon ana ganin fiye da ma’aikata 2,585 za su rasa ayyuansu a majalisar kasa da fadar shugaban kasa, a yadda abin yake ofishin shugaban kasa Muhammadu Buhari na da masu rike da mukaman siyasa 160 yayin da mataimakinsa Yemi Osinbajo ke da ma’aikata 80 wadanda ke taimaka masa a bangarori da dama.

A majalissar kasa kuma akwai ma’aikata na kaida 2,345 da suke yi wa ‘yan majalisa 469, sanatoci 109 ‘yan majaliisar wakilai 360, suna aiki ne a bangarori daban-daban don kawo wa ‘yan majalisar sauki a yayin db suka gudanar da ayyukansu. Ana iya samun kakrin mataimaka ga ‘yan majalisu in har shi dan majalisar yana neman karin masu taimakama masa wadnda kuma suna cikin wadanda za su rasa aiki a wannan lokacin na sauyin gwamnati.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Guraben AikiSauyin GwamnatiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Farfado Da Burin Rage Amfani Da Tsabar Kudi A Tsakanin Al’umma

Next Post

Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

17 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

19 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

21 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

23 hours ago
Next Post
Sauyin Kudi: Tunibu Ya Kutsa Kai Wurin Taron Gaggawa Da APC Ta Kira Gwamnoninta A Abuja

Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.