ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya

by Bello Hamza
3 years ago
Sauyin Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A daidai lokacin da gwamnatin Muhammadu Buhari ke shirye-shirye mika mulki ga sabuwar gwamnati ma’aikata musamman masu rike da mukaman siyasa suna fuskantar rasa ayyukansu saboda sabbin nade-naden da za a yi a sabuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, kamar dai yadda binciken da LEADERSHIP HAUSA ta yi.

Duk da yake lamarin rasa aiki ba wani sabon abu ba ne, musamman ganin gwamnati mai kamawa za ta nada mutanen ta ne da za su yi aiki tare, amma fargarbar da ke tattare da rasa aiki ya kara kamari a tsakanin masu rike da mukaman siyasa a wannan lokacin.

  • Wasu Ke Neman Bata Mana Suna Kan Rikicin Shugabancin APGA – INEC
  • Gwamnati Ta Amince Da Sabbin Manufofin Bunkasa Samar Da Motoci A Nijeriya 

Binciken mu ya nuna cewa, rasa ayyukan zai dangantaka ne da irin tsare-tsaren da yadda sabuwar gwamnatin ta shirya gudanarwa da ayukan da za ta sa a gaba da zaran an rantsar da ita.

A baya, wasu sabbin gwamnatin da aka yi su kan zabi kawar da kowa ne da ya yi aiki da gwamnati mai barin gado wanda hakan ke haifar da rashin ayyukan yi mai dimbin yawa yayin da wasu gamnatin ke zabar samar da canjji a sannu da hankali har a kai ga canza wadanda suka yi wa tsohuwar gwamnati aiki a samar da sabbin mutane da za su yi aiki da sabuwar gwamnatin gaba daya.

Lamarin a wannan lokacin ya za da sabon salo musamman ganin kasar na fuskantar matsalolin tattalin arziki, abin da ya sa ake ganin gwamnatin na Bola Tinubu za ta nemai aiwatar da rahoton kwamitjn nan na Stebe Oronsaye wanda ya bayar da shawarar sake fasalin ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya, akalla kwamitin ya nemi a hada wasu ma’aikatu a wuri daya ko kuma a rusa wasu ma’aikatan ba tare da wata lokaci ba, wannan aiki kuma ana ganin zai shafi akalla ma’aikata fiye 102 yayin da kuma za a umarci wasu ma’aikatan su fuskanci nema wa kansu kudaden shiga.

Nijeriya na ci gaba da farfadowa daga rikicin karayar tattalin arziki da aka fuskanta a tsakanin shekarar 2016 zuwa 2017, da matsalar da cutar korona ya haifar a shekarar 2020 wadanda suka tagayyara tsarin tattalin arzikin kasa.

Yayin da gwanmati ke kokarin ganijn ta sauke nauyin da ke a kanta na biyan albashi da sauransu, ta kuma tilastawa kanta karbar basuka don gudanar da manyan ayyuka akwai manyan fargaban cewa nauyi zai yi wa gwamnati mai kamawa yawa ta yadda ba za ta iya biyan hakokin da ke a kan ta ba na al’umma Nijeriya kamar yadda ta yi alkawari.

In har gwfamnati mai kamawa ta bata yanke shawarar rage ma’akatun gwamnati, hakan zai kai ga rasa ayyukan yi a tsakanijn ‘yan Nijeriya, abin kuma da zai fi shafar masu mukaman siyasa saboda ana ganin su a matsayin cima zaune.

Amma kuma ga dukkan masu mukaman siyasa ne za a iya kira da cima zaune ba, musamman ganin ana iya amfani da su wajen tabbatar da ayyukan gwamnati na cigaba daga gwamnatin da ke barin gado zuwa gwamnatin mai kamawa.

Abin kura kuma ba wai rasa aikin zai tsaya ne kawai a ikajn masu rike da mukaman siyasa kawai ba ne, lamarin zai iya sahafar wasu ma’aikatun gwamnati da ke fiuskantar matsalar rashin kudaden gudanarwa.

A wannan karon ana ganin fiye da ma’aikata 2,585 za su rasa ayyuansu a majalisar kasa da fadar shugaban kasa, a yadda abin yake ofishin shugaban kasa Muhammadu Buhari na da masu rike da mukaman siyasa 160 yayin da mataimakinsa Yemi Osinbajo ke da ma’aikata 80 wadanda ke taimaka masa a bangarori da dama.

A majalissar kasa kuma akwai ma’aikata na kaida 2,345 da suke yi wa ‘yan majalisa 469, sanatoci 109 ‘yan majaliisar wakilai 360, suna aiki ne a bangarori daban-daban don kawo wa ‘yan majalisar sauki a yayin db suka gudanar da ayyukansu. Ana iya samun kakrin mataimaka ga ‘yan majalisu in har shi dan majalisar yana neman karin masu taimakama masa wadnda kuma suna cikin wadanda za su rasa aiki a wannan lokacin na sauyin gwamnati.

Sauyin Gwamnati
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Sauyin Kudi: Tunibu Ya Kutsa Kai Wurin Taron Gaggawa Da APC Ta Kira Gwamnoninta A Abuja

Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.