• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tasa Ƙeyar Dr. Idris Kan Zargin Kalaman Batanci Ga Manzon Allah

Za Mu Bi Masa Kadinsa, In Ji Almajiran Malamin

by yahuzajere
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tasa Ƙeyar Dr. Idris Kan Zargin Kalaman Batanci Ga Manzon Allah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotu ta aike da fitaccen malamin addinin a jihar Bauchi, Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi gidan yari bisa zarginsa kalaman tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiya.

Malamin wanda ya amsa gayyatar ‘yansanda a ranar Litinin daga bisani suka gurfanar da shi a gaban kotu bisa zargin tada zaune tsaye.

  • Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

Bayanan da ke zuwa mana na cewa ‘yansandan sun gurfanar da shi ne a gaban kotun Majistire ta 1.

Kotun ta tura shi zuwa gidan yarin kafin daga bisani a cigaba da sauraron karar da ‘yansanda suka shigar da shi a gobe Talata.

Da yake tabbatar da kamun da aka yi wa malamin, Shugaban kungiyar, Majalisar Matasa Masu Neman Hadin Kan Malamai Da Cigaban Al’ummar Jihar Bauchi, Yusuf A. Jibrin, ya bayyana cewar malamin ya je wajen ‘yansanda domin amsa gayyatar da suka yi masa ne amma daga bisani suka gurfanar da shi a gaban kotu.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Ya ce: “Na san da gayyatar da aka yi wa Malam daga hukumar ‘yansanda wanda a yau da safe (Litinin) aka tabbatar mana da cewa Malam ya amsa wannan gayyatar. A da kam ma mun shirya har da ni muka ce za mu je mu yi masa rakiya. Amma da muka yi waya da Allaramma sai ya ce mana a’a malam ya ce bai bukatar kowa ya je. Zai je shi kadai da direba da Malam Ya’u.

“Dazu kuma sai shi Allaramma ya kirani yake ce min an kai Malam gidan Yari. Yake ce min har an kaishi kotu, kotu kuma ta turashi gidan yari.”

Yusuf ya ce, dukkanin abun da ake cajin malamin nasu a kai abu ne da ya shafi akidarsu, “Wannan maganar da malam ya yi akidarmu ne a kai kuma muke fatan Allah ya karbi rayukanmu, kuma manufarmu daya kuma a kanta muke.”

A cewarsa, malaminsu ya koyar da su zaman lafiya da kwanciyar hankali, don haka za su bi dukkanin matakan da suka dace a doron shari’a wajen nema wa malaminsu hakkinsa.

Shugaban, ya bayyana cewar su na ta kokarin kwantar wa almajiran malamin hankali da su kwantar da hankalinsu yayin da ake cigaba da bin matakan da suka dace wajen ganin malamin ya samu ‘yanci.

“Muna kira ga mutanenmu da su kasance cikin zaman lafiya kuma za mu bi lamarin a bisa tsarin doka domin mu tabbatar mun bi kadin abun da aka mana,” Yusuf A. Jibrin ya shaida.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa, a kwanakin baya ne Malamin na Ahlul Sunnah Dakta IdrisAbdul’aziz Dutsen Tanshi ya yi furucin cewa ‘…Ko taimakon Manzon Allah ma ba su bukata. Kafin nan ya jero sunayen wasu Shehunnan Darika inda ya nuna cewa ba a neman agajinsu a yayin neman taimako ko a lokacin da ake cikin yanayi na musifa.

Bayan yin jawabin nan nasa ne wasu ke ganin rashin ladabi wajen shigo da Manzon Allah (SAW) cikin misalinsa wanda kai tsaye wasu suka nuna hakan da rashin kimanta Manzon Allah. A kan hakan, hukumar shari’a ta jihar Bauchi ta aike da wasikar gayyata ga Malam Idris domin ya bayyana a gaban malamai domin wanke kansa ko kare kansa sai dai bayan caa da malaman da ke goyan bayansa suka yi hakan ya gagara ba tare da an samu yin wannan mukabalar ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Ya Kamata G7 Ta Bukaci Amurka Ta Daina Yunkurin Raba Duniya Gida 2

Next Post

Xi Ya Amsa Wasikar Daliban Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

19 minutes ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

2 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

4 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

4 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

9 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

20 hours ago
Next Post
Xi Ya Amsa Wasikar Daliban Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya

Xi Ya Amsa Wasikar Daliban Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.