• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Lokutan mika mulki na shugaban kasa lokuta ne na farin ciki a tsakanin al’umma sannan kuma lokuta ne mafi damuwa ga masu mika madafun iko. Lokutan mika mulki suna da wata alaka da damuwa da dimauta mai cike da dimbin rikici da kalubale.

Shugaban kasa mai barin gado, ba wai kawai zai cigaba da jagorancin kasa ba ne, dole ne ya fara shirya mika ragamar shugabancin ga sabon shugaba mai jiran gado da tawagarsa.

  • Hilda Bassey: ‘Yar Nijeriya Da Ta Kafa Tarihi A Fannin Girki A Duniya

A wannan lokaci, shugaba mai barin gado bai da wata cikakkiyar karfin guiwa sabida kusan duk al’amuran mulki da kwarjini a wurin Jama’a ya fara komawa wurin shugaba mai jiran gado.

Shugaban kasa da tawagarsa za su fara fuskantar halin da ake ji na rabuwa da mulki musamman na fara rasa abokai masu son alaka da makusanta kujerar shugaban kasa.

Ziyarar ban-girma da aka saba kaiwa shugaban kasa mai ci a sannu a hankali sai ta fara gushewa ta koma bangaren zababben shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Wadannan halaye na siyasa – fara janyewa daga shugaba mai barin gado zuwa mai jiran gado, a karshe dai duk za su dusashe da zarar an mika mulki. Wannan rana ta bikin mika mulki ga shugaban kasa a Nijeriya, za a yi ta a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A Nijeriya, daga 1999 zuwa yau, an yi bukukuwan mika mulki sau shida, amma sau uku daga shugaban kasa zuwa wani shugaba – Obasanjo zuwa ‘Yar’Adua/ Jonathan, Jonathan zuwa Buhari, yanzu kuma Buhari zuwa Tinubu.

Akwai nau’o’i biyu ne na mika mulki na shugaban kasa: akwai daga shugaban kasa zuwa shugaban kasa a karkashin jam’iyya daya sai kuma wanda ba a karkashin jam’iyya daya ba suka fito. Duka wadannan nau’ikan a Nijeriya mun dandanasu bisa tsarin dimokuradiyya, wannan alama ce na Nijeriya tana kan turbar Dimokuradiyya.

Kowane canji yana haifar da kalubale da firgici daban-daban da kiyayya. Amma kuma a wannan sauyin na halin yanzu akwai aminci sosai fiye da yadda aka saba ganin sabani tsakanin zababbe da mai barin gado – Shugaba Buhari na jam’iyyar APC zai mikawa zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC mulki.

Wannan shi ne bangare mafi sauki na wannan mika mulki na shugaban kasa da ke cike da cece-kuce kuma ya raba ra’ayoyin jama’a zuwa mabambantan ra’ayi – wasu suna kira da a dage rantsar da shugaban kasa sabida dalilai daban-daban na zato, wasu kuma suna nan kan cewa, babu wani dalili da zai hana rantsar da zababben shugaban kasa, bisa ga ka’ida da tanade-tanaden kundin tsarin mulkin mu. Duk suna da hakkin ra’ayinsu amma dole ne dokar kasa ta yi rinjaje.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
Manyan Labarai

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
Next Post
Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.