ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

by Sulaiman
3 years ago
Tinubu

Lokutan mika mulki na shugaban kasa lokuta ne na farin ciki a tsakanin al’umma sannan kuma lokuta ne mafi damuwa ga masu mika madafun iko. Lokutan mika mulki suna da wata alaka da damuwa da dimauta mai cike da dimbin rikici da kalubale.

Shugaban kasa mai barin gado, ba wai kawai zai cigaba da jagorancin kasa ba ne, dole ne ya fara shirya mika ragamar shugabancin ga sabon shugaba mai jiran gado da tawagarsa.

  • Hilda Bassey: ‘Yar Nijeriya Da Ta Kafa Tarihi A Fannin Girki A Duniya

A wannan lokaci, shugaba mai barin gado bai da wata cikakkiyar karfin guiwa sabida kusan duk al’amuran mulki da kwarjini a wurin Jama’a ya fara komawa wurin shugaba mai jiran gado.

ADVERTISEMENT

Shugaban kasa da tawagarsa za su fara fuskantar halin da ake ji na rabuwa da mulki musamman na fara rasa abokai masu son alaka da makusanta kujerar shugaban kasa.

Ziyarar ban-girma da aka saba kaiwa shugaban kasa mai ci a sannu a hankali sai ta fara gushewa ta koma bangaren zababben shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Wadannan halaye na siyasa – fara janyewa daga shugaba mai barin gado zuwa mai jiran gado, a karshe dai duk za su dusashe da zarar an mika mulki. Wannan rana ta bikin mika mulki ga shugaban kasa a Nijeriya, za a yi ta a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A Nijeriya, daga 1999 zuwa yau, an yi bukukuwan mika mulki sau shida, amma sau uku daga shugaban kasa zuwa wani shugaba – Obasanjo zuwa ‘Yar’Adua/ Jonathan, Jonathan zuwa Buhari, yanzu kuma Buhari zuwa Tinubu.

Akwai nau’o’i biyu ne na mika mulki na shugaban kasa: akwai daga shugaban kasa zuwa shugaban kasa a karkashin jam’iyya daya sai kuma wanda ba a karkashin jam’iyya daya ba suka fito. Duka wadannan nau’ikan a Nijeriya mun dandanasu bisa tsarin dimokuradiyya, wannan alama ce na Nijeriya tana kan turbar Dimokuradiyya.

Kowane canji yana haifar da kalubale da firgici daban-daban da kiyayya. Amma kuma a wannan sauyin na halin yanzu akwai aminci sosai fiye da yadda aka saba ganin sabani tsakanin zababbe da mai barin gado – Shugaba Buhari na jam’iyyar APC zai mikawa zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC mulki.

Wannan shi ne bangare mafi sauki na wannan mika mulki na shugaban kasa da ke cike da cece-kuce kuma ya raba ra’ayoyin jama’a zuwa mabambantan ra’ayi – wasu suna kira da a dage rantsar da shugaban kasa sabida dalilai daban-daban na zato, wasu kuma suna nan kan cewa, babu wani dalili da zai hana rantsar da zababben shugaban kasa, bisa ga ka’ida da tanade-tanaden kundin tsarin mulkin mu. Duk suna da hakkin ra’ayinsu amma dole ne dokar kasa ta yi rinjaje.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.