• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wai Kasar Sin Na Yin Matsin Tattalin Arziki? Lallai Mataki Ne Da Amurka Ta Dauka Don Dakile Ta

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wai Kasar Sin Na Yin Matsin Tattalin Arziki? Lallai Mataki Ne Da Amurka Ta Dauka Don Dakile Ta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne aka rufe taron kolin kungiyar G7 na tsawon yini uku a birnin Hiroshima na kasar Japan. Sai dai hadaddiyar sanarwar da taron ya fitar ta kara wa batutuwan da suka shafi kasar Sin gishiri, inda mahalarta taron suka yi barazanar daukar matakai na tinkarar abin da suka kira wai “matsin tattalin arziki”, matakin da ya bayyana yadda kasashen yammacin duniya da ke karkashin jagorancin kasar Amurka suke yin amfani da kungiyar G7 wajen yin babakere da ma neman dakile kasar Sin.

A zahiri dai, Amurka ce kasar da ke yin matsin tattalin arziki, duba da yadda ta sha daukar matakai na sanya takunkumi da kayyade fitar ko shigar da kayayyaki da kara sanya harajin kwastan da sauransu, don yi wa sauran kasashe matsin tattalin arziki, baya ga kuma yadda take tilasta yin amfani da dokokinta na cikin gida a kan sauran kasashe, da ma tilasta wasu kasashe katse huldar tattalin arziki da su. Hakika matakan da ta dauka na matsin tattalin arziki ba sa lisaftuwa, wadanda suka lalata tsarin samar da kayayyaki na duniya tare da jawo baraka ga kasuwar duniya.

  • Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

Ko da kawayenta da ke cikin kungiyar G7 ma ba su tsira daga matakanta na matsin tattalin arziki ba. In mun duba tarihi, kamfanin Toshiba na Japan da Siemens na Jamus da kuma Alstom na Faransa, wadanda dukkaninsu kamfanoni ne na kasashe kawayen kasar Amurka, duk sun fuskanci irin matakan da Amurka ta dauka, sakamakon yadda suka zama kalubale gare ta. Saboda a ganin kasar Amurka, moriya ce kawai za ta dore a maimakon zumunta.

Sai dai abin takaici ne yadda su kasashe mambobi kungiyar G7 da Amurka ta yi musu illa, har yanzu suke hada kai da Amurka din suke yi wa wasu illar da suka taba fuskanta.

‘Yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka sun kware wajen jirkita gaskiya bisa tasirinsu na iya magana, kuma zancen nan na wai “matsin tattalin arziki” mataki ne da Amurka ta dauka don takura wa kasar Sin. Sanin kowa ne kasar Sin na nacewa ga bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, wadda kuma take tsayawa tsayin daka a kan manufar bude kofa ga juna don cin moriyar juna. A cikin shekaru 10 da suka wuce, gudummawar da ta samar wa bunkasuwar tattalin arzikin duniya ta zarce wadda kasashen G7 suka bayar baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Hasashen da bankin duniya ya yi ya kuma shaida cewa, ya zuwa shekarar 2030, shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar za ta fitar da mutanen duniya miliyan 7.6 daga matsanancin talauci. Baya ga haka, manyan ababen more rayuwa da kasar Sin ke ginawa a sassan duniya na taimakawa kasashe daban daban raya tattalin arzikinsu. Da hakan muke iya gano cewa,kasar Sin tana samar da zarafi da ci gaba ga duniya a maimakon kalubale da barazana.

Kasancewarsu kasashe masu sukuni, ya kamata kasashen G7 su kara mai da hankali a kan yadda za su taimaka ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma bunkasuwa a duniya, a maimakon neman lalata zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya da ma dalike ci gaban sauran kasashe.(Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban DRC Zai Ziyarci Kasar Sin

Next Post

Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

15 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

16 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

18 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

18 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

20 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

22 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi

Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul'aziz Dutsen Tanshi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.