ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wai Kasar Sin Na Yin Matsin Tattalin Arziki? Lallai Mataki Ne Da Amurka Ta Dauka Don Dakile Ta

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A jiya ne aka rufe taron kolin kungiyar G7 na tsawon yini uku a birnin Hiroshima na kasar Japan. Sai dai hadaddiyar sanarwar da taron ya fitar ta kara wa batutuwan da suka shafi kasar Sin gishiri, inda mahalarta taron suka yi barazanar daukar matakai na tinkarar abin da suka kira wai “matsin tattalin arziki”, matakin da ya bayyana yadda kasashen yammacin duniya da ke karkashin jagorancin kasar Amurka suke yin amfani da kungiyar G7 wajen yin babakere da ma neman dakile kasar Sin.

A zahiri dai, Amurka ce kasar da ke yin matsin tattalin arziki, duba da yadda ta sha daukar matakai na sanya takunkumi da kayyade fitar ko shigar da kayayyaki da kara sanya harajin kwastan da sauransu, don yi wa sauran kasashe matsin tattalin arziki, baya ga kuma yadda take tilasta yin amfani da dokokinta na cikin gida a kan sauran kasashe, da ma tilasta wasu kasashe katse huldar tattalin arziki da su. Hakika matakan da ta dauka na matsin tattalin arziki ba sa lisaftuwa, wadanda suka lalata tsarin samar da kayayyaki na duniya tare da jawo baraka ga kasuwar duniya.

  • Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

Ko da kawayenta da ke cikin kungiyar G7 ma ba su tsira daga matakanta na matsin tattalin arziki ba. In mun duba tarihi, kamfanin Toshiba na Japan da Siemens na Jamus da kuma Alstom na Faransa, wadanda dukkaninsu kamfanoni ne na kasashe kawayen kasar Amurka, duk sun fuskanci irin matakan da Amurka ta dauka, sakamakon yadda suka zama kalubale gare ta. Saboda a ganin kasar Amurka, moriya ce kawai za ta dore a maimakon zumunta.

ADVERTISEMENT

Sai dai abin takaici ne yadda su kasashe mambobi kungiyar G7 da Amurka ta yi musu illa, har yanzu suke hada kai da Amurka din suke yi wa wasu illar da suka taba fuskanta.

‘Yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka sun kware wajen jirkita gaskiya bisa tasirinsu na iya magana, kuma zancen nan na wai “matsin tattalin arziki” mataki ne da Amurka ta dauka don takura wa kasar Sin. Sanin kowa ne kasar Sin na nacewa ga bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, wadda kuma take tsayawa tsayin daka a kan manufar bude kofa ga juna don cin moriyar juna. A cikin shekaru 10 da suka wuce, gudummawar da ta samar wa bunkasuwar tattalin arzikin duniya ta zarce wadda kasashen G7 suka bayar baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Hasashen da bankin duniya ya yi ya kuma shaida cewa, ya zuwa shekarar 2030, shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar za ta fitar da mutanen duniya miliyan 7.6 daga matsanancin talauci. Baya ga haka, manyan ababen more rayuwa da kasar Sin ke ginawa a sassan duniya na taimakawa kasashe daban daban raya tattalin arzikinsu. Da hakan muke iya gano cewa,kasar Sin tana samar da zarafi da ci gaba ga duniya a maimakon kalubale da barazana.

Kasancewarsu kasashe masu sukuni, ya kamata kasashen G7 su kara mai da hankali a kan yadda za su taimaka ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma bunkasuwa a duniya, a maimakon neman lalata zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya da ma dalike ci gaban sauran kasashe.(Lubabatu)

 

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi

Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul'aziz Dutsen Tanshi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.