ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

by CMG Hausa
3 years ago
Hiroshima

A kwanakin nan, an gudanar da manyan tarukan koli guda biyu kusan a lokaci guda, wato taron kolin kasar Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya wanda aka gudanar a birnin Xi’an na kasar Sin, birnin dake zama mafarin hanyar siliki, da kuma taron kolin kungiyar G7, wanda aka gudanar a birnin Hiroshima, birni na farko a duniya da aka kai masa harin nukiliya, hakan nan kuma tarukan biyu sun bambanta sosai bisa la’akari da abubuwan da suke neman cimmawa.

Taron kolin kasar Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya wanda aka kammala shi ba da jimawa ba, ya mai da hankali a kan karfafa hadin gwiwa don tinkarar kalubale, kuma manufar taron shi ne karfafa hadin kai a maimakon yin fito na fito.

  • Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin

Kamar dai yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a jawabinsa cewa, duniya na fatan ganin tabbatar da kwanciyar hankali da ci gaba da jituwa da hadewa da juna a tsakiyar Asiya, ya kamata a gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakanin Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya, kuma ya kamata kasashen su tsaya kan taimakon juna da tabbatar da ci gaban juna da tsaronsu na bai daya da sada zumunta da juna daga zuriya zuwa zuriya.

ADVERTISEMENT

Haka nan kuma ya shaida yadda kasar Sin ke cudanya da kasashen biyar din da ke tsakiyar Asiya bisa tushen zaman daidaito, kuma ba domin dakile wata kasa ba suke hulda da juna.

Taron na yini biyu ya cimma gagaruman nasarori, kuma babu shakka ya shaida ainihin ma’anar cudanyar kasa kasa, tare da kiyaye tsari da adalci a duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

A daya bangare kuma, taron kolin G7 da har yanzu ke gudana a birnin Hiroshima, yana mai da hankali a kan haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin kasashen duniya, wato su kulla kawance don yin fito na fito da wasu kasashe. Kasar Japan mai masaukin baki tana amfani da damarta ta karbar bakuncin taron, don neman kulla kawance da sauran kasashen kungiyar, a yunkurin tinkarar abin da take kira wai “barazana daga Rasha da Sin da kuma Koriya ta arewa”, a sa’i daya kuma, tana neman goyon baya daga kawayen nan nata a kan batun zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin tekun Pasifik. Ita kuma kasar Amurka ma burinta a bayyane ne, wato tana ci gaba da neman rura wutar rikicin Ukraine, tare da karfafa kawancenta da kasashen G7 wajen tinkarar kasar Sin. Da haka, muke iya gano cewa, manufar taron G7 shi ne su karfafa kawancensu don dakile sauran kasashe.

In mun kwatanta tarukan biyu, cikin sauki za mu gane cewa, tarukan biyu sun bambanta sosai daga dalilan gudanar da su da ma burin da ake neman cimmawa. Taron da aka gudanar a birnin Xi’an an gudanar da shi ne sabo da neman ci gaba na bai daya, don haka ma, abin da aka tattauna a gun taron shi ne ta yaya za a tabbatar da ci gaban kasashen.

A sa’i daya kuma, taron da aka gudanar a Hiroshima ya shaida yadda kasashen G7 suke da ra’ayin nan na samun ci gaba daga faduwar wani, don haka ma, sun fi mai da hankali a kan yadda za su kulla kawance da juna don yin fito na fito da wasu.

Daga Xi’an zuwa Hiroshima, tarukan biyu tamkar wani madubi ne dake haskakawa kasashen duniya, don gano amsa idan sun kwatanta su. (Lubabatu Lei)

Hiroshima
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Next Post
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

…Yadda Daura Ke Haramar Tarbar Buhari – Alhaji Saleh

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.