• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan, an gudanar da manyan tarukan koli guda biyu kusan a lokaci guda, wato taron kolin kasar Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya wanda aka gudanar a birnin Xi’an na kasar Sin, birnin dake zama mafarin hanyar siliki, da kuma taron kolin kungiyar G7, wanda aka gudanar a birnin Hiroshima, birni na farko a duniya da aka kai masa harin nukiliya, hakan nan kuma tarukan biyu sun bambanta sosai bisa la’akari da abubuwan da suke neman cimmawa.

Taron kolin kasar Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya wanda aka kammala shi ba da jimawa ba, ya mai da hankali a kan karfafa hadin gwiwa don tinkarar kalubale, kuma manufar taron shi ne karfafa hadin kai a maimakon yin fito na fito.

  • Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin

Kamar dai yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a jawabinsa cewa, duniya na fatan ganin tabbatar da kwanciyar hankali da ci gaba da jituwa da hadewa da juna a tsakiyar Asiya, ya kamata a gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakanin Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya, kuma ya kamata kasashen su tsaya kan taimakon juna da tabbatar da ci gaban juna da tsaronsu na bai daya da sada zumunta da juna daga zuriya zuwa zuriya.

Haka nan kuma ya shaida yadda kasar Sin ke cudanya da kasashen biyar din da ke tsakiyar Asiya bisa tushen zaman daidaito, kuma ba domin dakile wata kasa ba suke hulda da juna.

Taron na yini biyu ya cimma gagaruman nasarori, kuma babu shakka ya shaida ainihin ma’anar cudanyar kasa kasa, tare da kiyaye tsari da adalci a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

A daya bangare kuma, taron kolin G7 da har yanzu ke gudana a birnin Hiroshima, yana mai da hankali a kan haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin kasashen duniya, wato su kulla kawance don yin fito na fito da wasu kasashe. Kasar Japan mai masaukin baki tana amfani da damarta ta karbar bakuncin taron, don neman kulla kawance da sauran kasashen kungiyar, a yunkurin tinkarar abin da take kira wai “barazana daga Rasha da Sin da kuma Koriya ta arewa”, a sa’i daya kuma, tana neman goyon baya daga kawayen nan nata a kan batun zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin tekun Pasifik. Ita kuma kasar Amurka ma burinta a bayyane ne, wato tana ci gaba da neman rura wutar rikicin Ukraine, tare da karfafa kawancenta da kasashen G7 wajen tinkarar kasar Sin. Da haka, muke iya gano cewa, manufar taron G7 shi ne su karfafa kawancensu don dakile sauran kasashe.

In mun kwatanta tarukan biyu, cikin sauki za mu gane cewa, tarukan biyu sun bambanta sosai daga dalilan gudanar da su da ma burin da ake neman cimmawa. Taron da aka gudanar a birnin Xi’an an gudanar da shi ne sabo da neman ci gaba na bai daya, don haka ma, abin da aka tattauna a gun taron shi ne ta yaya za a tabbatar da ci gaban kasashen.

A sa’i daya kuma, taron da aka gudanar a Hiroshima ya shaida yadda kasashen G7 suke da ra’ayin nan na samun ci gaba daga faduwar wani, don haka ma, sun fi mai da hankali a kan yadda za su kulla kawance da juna don yin fito na fito da wasu.

Daga Xi’an zuwa Hiroshima, tarukan biyu tamkar wani madubi ne dake haskakawa kasashen duniya, don gano amsa idan sun kwatanta su. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hilda Bassey: ‘Yar Nijeriya Da Ta Kafa Tarihi A Fannin Girki A Duniya

Next Post

…Yadda Daura Ke Haramar Tarbar Buhari – Alhaji Saleh

Related

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

5 hours ago
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

6 hours ago
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

7 hours ago
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

8 hours ago
Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
Daga Birnin Sin

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

9 hours ago
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

1 day ago
Next Post
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

…Yadda Daura Ke Haramar Tarbar Buhari – Alhaji Saleh

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.