• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

by Sulaiman
2 years ago
tafiye-tafiye

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta sake jaddada kira ga kafafen yada labarai su rubanya kwazonsu wajen bayar da rahotannin da suka kamata a kan tafiye-tafiyen kasashen waje ta barauniyar hanya da kuma fadakar da jama’a game da hadarin da ke tattare da hakan.

Hukumar ta yi kiran ne a yayin gudanar da wani taron wayar da kai ga ‘yan jaridu da ya gudana a Abuja a ranar Litinin, a otel din Reiz Continental.

  • Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu

Shugaban Hukumar, CGI Isah Idris Jere ya yi kiran ta bakin wakiliyarsa a taron, Babbar Jami’a Mai Kula da Sashen Tafiye-tafiye a shalkwatar hukumar, ACG Ngozi Odikpo. Wakiliyar ta gabatar da Makala a kan abubuwan da ya kamata ‘yan jarida su mayar da hankali a kai wajen bayar da rahotanninsu game da yadda jama’a ke kaura ta hanyar da ta dace da kuma masu bin barauniyar hanya, tana mai jaddada cewa, ya kamata kafafen yada labarai su rika hadawa da labarun mutanen da suka fada komar masu safarar bil’adama ba bisa ka’ida ba domin wayar da kan al’umma a kan mummunan hadarin da ke tattare da hakan.

Har ila yau, tsohon shugaban hukumar ta NIS, Muhammad Babandede wanda ya yi jawabi a kan batutuwan da suka shafi tafiye-tafiye da suka halasta da wadanda suka haramta, da kuma su kansu mutanen da ke tafiye-tafiyen, ya nuna akwai bukatar kafafen yada labarai su rika bayar da rahotannin da suka dace na kiyaye mutuncin Nijeriya, yana mai ba da misali da irin kalaman da ake amfani da su wajen bayar da rahotannin da suka shafi kasa domin wayar da kan ‘yan kasa.

Ya nemi a rika fada wa ‘yan kasa gaskiyar abin da yake faruwa ta hanyar ilmantarwa da kuma fadakar da su game da tafiye-tafiye da ke kan ka’ida da kuma wadanda suka saba.

LABARAI MASU NASABA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Kungiyar ‘Yan Jarida Masu Rubuta Labarun Tafiye-tafiyen Kasashen Waje ta Duniya (JIFORM) tare da hadin gwiwar Cibiyar Kula da Tafiye-tafiye ta Kasar Jamus (NGC) suka shirya taron a kan yadda za a inganta bayar da rahotannin da suka shafi tafiye-tafiye ba bisa ka’ida ba da hadarin hakan.

Wakazalika, Kwanturolan NIS na Jihar Ribas, CI James Sunday ya gabatar da makaloli biyu a wurin taron domin wayar da kan ‘yan jarida a kan hakkokin da suka rataya a wuyarsu na bayar da rahotannin tafiye-tafiyen da suka dace da wadanda suka saba wa doka.

Taron ya kuma samu halartar manyan baki daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da sauran kungiyoyi masu nasaba da kai-komon jama’a.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole
Labarai

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Next Post
‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.