ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

by Sulaiman
3 years ago
tafiye-tafiye

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta sake jaddada kira ga kafafen yada labarai su rubanya kwazonsu wajen bayar da rahotannin da suka kamata a kan tafiye-tafiyen kasashen waje ta barauniyar hanya da kuma fadakar da jama’a game da hadarin da ke tattare da hakan.

Hukumar ta yi kiran ne a yayin gudanar da wani taron wayar da kai ga ‘yan jaridu da ya gudana a Abuja a ranar Litinin, a otel din Reiz Continental.

  • Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu

Shugaban Hukumar, CGI Isah Idris Jere ya yi kiran ta bakin wakiliyarsa a taron, Babbar Jami’a Mai Kula da Sashen Tafiye-tafiye a shalkwatar hukumar, ACG Ngozi Odikpo. Wakiliyar ta gabatar da Makala a kan abubuwan da ya kamata ‘yan jarida su mayar da hankali a kai wajen bayar da rahotanninsu game da yadda jama’a ke kaura ta hanyar da ta dace da kuma masu bin barauniyar hanya, tana mai jaddada cewa, ya kamata kafafen yada labarai su rika hadawa da labarun mutanen da suka fada komar masu safarar bil’adama ba bisa ka’ida ba domin wayar da kan al’umma a kan mummunan hadarin da ke tattare da hakan.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, tsohon shugaban hukumar ta NIS, Muhammad Babandede wanda ya yi jawabi a kan batutuwan da suka shafi tafiye-tafiye da suka halasta da wadanda suka haramta, da kuma su kansu mutanen da ke tafiye-tafiyen, ya nuna akwai bukatar kafafen yada labarai su rika bayar da rahotannin da suka dace na kiyaye mutuncin Nijeriya, yana mai ba da misali da irin kalaman da ake amfani da su wajen bayar da rahotannin da suka shafi kasa domin wayar da kan ‘yan kasa.

Ya nemi a rika fada wa ‘yan kasa gaskiyar abin da yake faruwa ta hanyar ilmantarwa da kuma fadakar da su game da tafiye-tafiye da ke kan ka’ida da kuma wadanda suka saba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Kungiyar ‘Yan Jarida Masu Rubuta Labarun Tafiye-tafiyen Kasashen Waje ta Duniya (JIFORM) tare da hadin gwiwar Cibiyar Kula da Tafiye-tafiye ta Kasar Jamus (NGC) suka shirya taron a kan yadda za a inganta bayar da rahotannin da suka shafi tafiye-tafiye ba bisa ka’ida ba da hadarin hakan.

Wakazalika, Kwanturolan NIS na Jihar Ribas, CI James Sunday ya gabatar da makaloli biyu a wurin taron domin wayar da kan ‘yan jarida a kan hakkokin da suka rataya a wuyarsu na bayar da rahotannin tafiye-tafiyen da suka dace da wadanda suka saba wa doka.

Taron ya kuma samu halartar manyan baki daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da sauran kungiyoyi masu nasaba da kai-komon jama’a.

 

 

tafiye-tafiye
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.