ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

by Sulaiman
3 years ago
tafiye-tafiye

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta sake jaddada kira ga kafafen yada labarai su rubanya kwazonsu wajen bayar da rahotannin da suka kamata a kan tafiye-tafiyen kasashen waje ta barauniyar hanya da kuma fadakar da jama’a game da hadarin da ke tattare da hakan.

Hukumar ta yi kiran ne a yayin gudanar da wani taron wayar da kai ga ‘yan jaridu da ya gudana a Abuja a ranar Litinin, a otel din Reiz Continental.

  • Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu

Shugaban Hukumar, CGI Isah Idris Jere ya yi kiran ta bakin wakiliyarsa a taron, Babbar Jami’a Mai Kula da Sashen Tafiye-tafiye a shalkwatar hukumar, ACG Ngozi Odikpo. Wakiliyar ta gabatar da Makala a kan abubuwan da ya kamata ‘yan jarida su mayar da hankali a kai wajen bayar da rahotanninsu game da yadda jama’a ke kaura ta hanyar da ta dace da kuma masu bin barauniyar hanya, tana mai jaddada cewa, ya kamata kafafen yada labarai su rika hadawa da labarun mutanen da suka fada komar masu safarar bil’adama ba bisa ka’ida ba domin wayar da kan al’umma a kan mummunan hadarin da ke tattare da hakan.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, tsohon shugaban hukumar ta NIS, Muhammad Babandede wanda ya yi jawabi a kan batutuwan da suka shafi tafiye-tafiye da suka halasta da wadanda suka haramta, da kuma su kansu mutanen da ke tafiye-tafiyen, ya nuna akwai bukatar kafafen yada labarai su rika bayar da rahotannin da suka dace na kiyaye mutuncin Nijeriya, yana mai ba da misali da irin kalaman da ake amfani da su wajen bayar da rahotannin da suka shafi kasa domin wayar da kan ‘yan kasa.

Ya nemi a rika fada wa ‘yan kasa gaskiyar abin da yake faruwa ta hanyar ilmantarwa da kuma fadakar da su game da tafiye-tafiye da ke kan ka’ida da kuma wadanda suka saba.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Kungiyar ‘Yan Jarida Masu Rubuta Labarun Tafiye-tafiyen Kasashen Waje ta Duniya (JIFORM) tare da hadin gwiwar Cibiyar Kula da Tafiye-tafiye ta Kasar Jamus (NGC) suka shirya taron a kan yadda za a inganta bayar da rahotannin da suka shafi tafiye-tafiye ba bisa ka’ida ba da hadarin hakan.

Wakazalika, Kwanturolan NIS na Jihar Ribas, CI James Sunday ya gabatar da makaloli biyu a wurin taron domin wayar da kan ‘yan jarida a kan hakkokin da suka rataya a wuyarsu na bayar da rahotannin tafiye-tafiyen da suka dace da wadanda suka saba wa doka.

Taron ya kuma samu halartar manyan baki daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da sauran kungiyoyi masu nasaba da kai-komon jama’a.

 

 

tafiye-tafiye
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan
  • Sulaiman
    Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.