• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a jihar Kano ta ayyana cewa zargin kisan kai da hada kai wajen yin kisa da ake yi wa shugaban masu rinjaye na Majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa.

Da yake jagorantar hukunci kan bukatar da Doguwa ya shigar kan tauye masa hakki da ‘yanci da tsare shi ba bisa ka’ida ba da karamar kotu ta yi, Mai Shari’a Mohammed Yunusa, a ranar Litinin ya ce, babban Kotun Majistire ba ta da hurumin sauraron karar da ya shafi aikata manyan laifuka.

  • Ba Ni Da Hurumin Gurfanar Da Alhassan Doguwa —Antoni-Janar
  • Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Mai Shari’a Yunusa ya buga misali da sashi na 251 (1) da ya ce babbar Kotun tarayya ce kadai ke da ikon sauraron karar da ta shafi bindigu kamar dai irin tuhumar da aka shigar kan Ado Doguwa.

Sai dai Alkalin ya nanata cewa ba fa kawai don an amince da bada belin Doguwa shi ke nan hakan na nuni da cewa ya samu kariyar da ba zai fuskanci shari’a ba ne, Yunusa ya ce dole a bi komai bisa doka da ka’ida.

Lauyan Ado Doguwa, Nureini Jimoh, shi ne ya nema masa umarnin samun kariya kan ‘yancin dan adamtaka kamar yadda dokar kasa ta bayar da dama ga kowa.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Lauyan nasa ya yi ikirarin cewa ‘yansanda sun tsare Doguwa ba bisa ka’ida ba wanda hakan ya taba masa hakkinsa da ‘yancinsa kamar yadda dokokin mulkin kasa na 1999 suka bayar.

Kazalika, ya bukaci kotun ta ayyana cewar sauraron karar da kotun Majistire ta yi bai dacewa ba kuma ajingine shi tare da ayyana cewar hakan ya saba wa tsarin mulkin kasa domin ba ta da hurumin da karfin ikon sauraron irin wannan karar da suka shafi manyan laifuka.

Alkali Yunusa ya ce ‘yan kasa na da dama bisa tanade-tanaden doka sashi na 46 (1) na kundin tsarin mulkin kasa ta 1999 da su je kowace babban kotu domin kalubalantar yunkurin tauye musu hakkinsu.

Mai Shari’a Yunusa ya ce tun da farko ma Bai dace a tsare Doguwa a gidan yari ba domin ba a gabatar da karar da ake masa ta hanyoyin da suka dace ba, ya kara da cewa shigar da karar da ‘yan sanda suka yi a karamar kotu bai dace ba.

Don haka ne ya haramta wa ‘yansanda kamawa, musgunawa ko tsare Alhassan Doguwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DoguwaKotuZargin Kisan Kai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Lafiya Ta Duniya Ta Sake Yin Watsi Da Shawarar Dake Shafar Taiwan

Next Post

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

Related

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

3 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

4 hours ago
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami
Labarai

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

6 hours ago
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

7 hours ago
Next Post
NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.