• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Kogi ta ce wasu ‘yan bindiga sun kai wa ayarin motocin Gwamna Yahaya Bello hari a kan hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Ta ce an kai harin ne a kusa da wani sansanin sojin ruwa, mai tazarar kilomita kadan daga Lokoja, babban birnin jihar.

  • Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?
  • Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Kwamishinan yada labaran Jihar Kogi, Kingsley Fanwo ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Lokoja.

Fanwo ya yi zargin cewa ‘yan bindigar ‘yan barandan siyasa ne na wata jam’iyyar adawa ta SDP a jihar.

Kwamishinan ya ce lamarin da ya faru da misalin karfe 12:30 na rana, ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da suka hada da jami’an tsaro wanda aka kai su asibiti domin kula da lafiyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

“’Yan bindigar da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne na jam’iyyar SDP, da suka hango ayarin Bello suna tahowa, sai suka tare hanya suka fara harbinsu.

“Amma Alhamdulillahi gwamnanmu ya tsira ba tare da samun wani rauni ba.

“Wasu mataimakan tsaro da sauran masu taimaka wa gwamnan sun samu raunuka, kuma an garzaya da su asibiti domin kula da su.

“Muna kira ga jama’ar Kogi da su kwantar da hankalinsu domin jami’an tsaro suna bincike dk cafke ‘yan bindigar da suka kai harin,” in ji shi.

Fanwo ya ce gwamnatin jihar ba za ta amince da karya doka da oda ba amma za ta yi duk mai yiwuwa domin gurfanar da maharan a gaban kuliya.

A cewarsa, gwamnan ya yi gargadin cewa kada wani dan jam’iyyar APC ya shiga duk wani harin ramuwar gayya domin hakan na iya haifar da rashin tsaro.

Da yake mayar da martani, Mista Kunle Afolayo, mai taimaka wa dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Yakubu Ajaka, a fannin yada labarai, ya musanta zargin magoya bayan jam’iyyar ne suka kai harin.

“Shin zai yiwu jam’iyyar siyasa ta adawa ta kai wa gwamna hari haka?

“Muna kan hanyarmu ta zuwa fadar Maigari da ke Lokoja daga Koton Karfe a yammacin yau, sai ayarin motocin gwamnan da suka nufi Lokoja daga Abuja suka same mu a hanya, suka kai mana hari.

“Allah ya san gaskiya. Abin takaici ne yadda gwamnatin APC a Kogi ke amfani da karfin gwamnati a kanmu tare da yi mana kazafi kan laifin da suka aikata mana,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyariHariJami'an TsaroKogiMotociYahaya BelloYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Next Post

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Related

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

1 week ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

3 weeks ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

3 weeks ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

4 weeks ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

4 weeks ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

4 weeks ago
Next Post
Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.