• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

by Sadiq
2 years ago
Yahaya Bello

Gwamnatin Kogi ta ce wasu ‘yan bindiga sun kai wa ayarin motocin Gwamna Yahaya Bello hari a kan hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Ta ce an kai harin ne a kusa da wani sansanin sojin ruwa, mai tazarar kilomita kadan daga Lokoja, babban birnin jihar.

  • Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?
  • Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Kwamishinan yada labaran Jihar Kogi, Kingsley Fanwo ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Lokoja.

Fanwo ya yi zargin cewa ‘yan bindigar ‘yan barandan siyasa ne na wata jam’iyyar adawa ta SDP a jihar.

Kwamishinan ya ce lamarin da ya faru da misalin karfe 12:30 na rana, ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da suka hada da jami’an tsaro wanda aka kai su asibiti domin kula da lafiyarsu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

“’Yan bindigar da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne na jam’iyyar SDP, da suka hango ayarin Bello suna tahowa, sai suka tare hanya suka fara harbinsu.

“Amma Alhamdulillahi gwamnanmu ya tsira ba tare da samun wani rauni ba.

“Wasu mataimakan tsaro da sauran masu taimaka wa gwamnan sun samu raunuka, kuma an garzaya da su asibiti domin kula da su.

“Muna kira ga jama’ar Kogi da su kwantar da hankalinsu domin jami’an tsaro suna bincike dk cafke ‘yan bindigar da suka kai harin,” in ji shi.

Fanwo ya ce gwamnatin jihar ba za ta amince da karya doka da oda ba amma za ta yi duk mai yiwuwa domin gurfanar da maharan a gaban kuliya.

A cewarsa, gwamnan ya yi gargadin cewa kada wani dan jam’iyyar APC ya shiga duk wani harin ramuwar gayya domin hakan na iya haifar da rashin tsaro.

Da yake mayar da martani, Mista Kunle Afolayo, mai taimaka wa dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Yakubu Ajaka, a fannin yada labarai, ya musanta zargin magoya bayan jam’iyyar ne suka kai harin.

“Shin zai yiwu jam’iyyar siyasa ta adawa ta kai wa gwamna hari haka?

“Muna kan hanyarmu ta zuwa fadar Maigari da ke Lokoja daga Koton Karfe a yammacin yau, sai ayarin motocin gwamnan da suka nufi Lokoja daga Abuja suka same mu a hanya, suka kai mana hari.

“Allah ya san gaskiya. Abin takaici ne yadda gwamnatin APC a Kogi ke amfani da karfin gwamnati a kanmu tare da yi mana kazafi kan laifin da suka aikata mana,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Next Post
Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.