• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
BRICS

“Kasashen BRICS na kasance tamkar maganadiso, wanda ke ta jawo masu neman tabbatar da zaman lafiya da hadin gwiwa… Mu ma Venezuala, muna fatan zama daya daga cikin kasashe mambobin BRICS.”

Shugaban kasar ta Venezuala Nicolás Maduro Moros ne ya fadi haka a kwanan baya a gun taron manema labarai da aka shirya bayan ganawarsa da takwaransa na kasar Brazil.

  • Jami’in Afirka Ta Kudu: Jagororin Dukkan Kasashen BRICS Za Su Halarci Taron Kolin BRICS Din Na Bana

Daga ranar 1 zuwa 2 ga wata, an gudanar da taron ministocin wajen kasashen BRICS a birnin Cape Town na kasar Afirka ta kudu, kuma fadada mambobin kungiyar na daya daga cikin muhimman batutuwan da aka tattauna a gun taron.

Bayanai na cewa, kasashe da dama ciki har da kasashen Afirka irinsu Aljeriya da Masar, duk sun bayyana burinsu na zama mambobin kungiyar BRICS, kafin wannan kuma, wakilin musamman na gwamnatin kasar Afirka ta kudu mai kula da harkokin Asiya da gabas ta tsakiya da kuma kasashen BRICS, Anil Sooklal ya bayyana cewa, “Kusan muna samun sakwannin neman zama mambar BRICS a kowace rana.”
Amma me ya sa BRICS ke kara farin jini?
In mun yi nazari, za mu gano cewa, hakan ya faru ne sabo da na farko, kungiyar BRICS na jawo hankalinsu ne sabo da yadda take neman hadin gwiwa da ci gaba, a maimakon rarrabuwar kawuna da yin fito na fito da juna.

Ba kamar yadda Amurka da kawayenta na yammacin duniya su kan kulla kawance ne don su tinkari wani, tsarin BRICS tun farkon kafuwarsa yana mai da hankali ne a kan inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa. A sa’i daya kuma, ba ya da niyyar yin fito na fito da kasashen yamma ko kuma maye gurbinsu.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Na biyu kuma, kasashen BRICS na dukufa a kan daidaita tsarin gudanar da harkokin duniya da ma kiyaye moriyar kasashe masu tasowa, sakamakon yadda kasashe masu tasowa ke fuskantar karancin wakilci da ma jin muryarsu a harkokin duniya. Tun kafa shi, tsarin na BRICS ya yi ta kokarin fito da muryar kasashe masu tasowa a duniya da kuma kare moriyarsu ta bai daya.

In mun dauki misali da asusun ba da lamuni na duniya(IMF), wanda kasancewarsa muhimmiyar hukumar kula da hada-hadar kudi ta duniya, amma kuma ta dade tana wakiltar kasashen yamma ne kawai.

Sai dai bisa kwaskwarima da aka sha yiwa asusun, tsarin BRICS ya kyautata wakilcin kasashe da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa a hukumar ta IMF.

A gun taron ministocin wajen BRICS da aka gudanar a wannan karo kuma, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Ma Zhaoxu ma ya sake jaddada cewa, ya kamata a kara wakilcin kasashe masu tasowa tare da kara jin muryarsu a harkokin duniya.

Na uku, BRICS na mai da hankali ne a kan cimma hakikanan nasarori da za su amfanawa kasashe masu tasowa.

In mun dauki misali da bankin NDB da kasashen BRICS suka kafa, wanda ya kasance banki na tsakanin kasa da kasa na farko da kasashe masu tasowa suka kafa, wanda tun kafuwarsa a shekaru 7 da suka wuce har zuwa yanzu, rancen kudin da ya samar har ya kai dala biliyan 32, wanda aka zuba su a fannonin bunkasa ababen more rayuwa da ma wasu ayyuka na tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen BRICS.

Musamman ma a lokacin da aka fuskanci annobar Covid-19, Bankin ya samar da kudin agajin gaggawa na dala biliyan 10 ga kasashe mambobin BRICS.

Yadda karin kasashe ke neman zama mambobin BRICS ya shaida mana bukatu na bai daya na kasashe masu tasowa, wato yin hadin gwiwa da juna don tabbatar da bunkasuwar juna, da kara tabbatar da adalcin tsarin duniya.(Lubabatu Lei)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
Daga Birnin Sin

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Next Post
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.