• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gobe ranar teku ce ta kasa da kasa karo na 15, babban taron MDD karo na 63 ya tsai da ranar 8 ga watan Yunin kowace shekara ranar teku ta kasa da kasa, don jan hankalin duniya muhimmancin kiyaye teku, wanda ke da babbar ma’ana ga bunkasuwar al’umma.

Amma a abin takaici ne, albarkacin wannan muhimmiyar rana, kasar Japan har yanzu tana kare aniyarta ta zuba ruwan dagwalon nukiliya ta tashar nukiliya ta Fukushima cikin teku bisa son kanta. Kwanan nan, kafar NHK ta kasar Japan ta ba da labarin cewa, an riga an fara zuba ruwan teku cikin bututun da ruwan dagwalon nukiliya zai bi a Fukushima.

  • An Bude Taron Kasa Da Kasa Na Baje Kolin Harkokin Al’adu A Shenzhen

Shirin nan na Japan ya jawo suka daga gida da ma waje, sai dai gwamnatin Japan ta yi ta neman wanke kanta ta kowa ce hanya.

Gwamnatin Japan ta ce ruwan dagwalon ba zai kawo illa ga muhallin teku ba, amma ko hakan gaskiya ne? A hakika, ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Kamfanin samar da wutar lantarki na Tokyo ya ba da wani rahoto a ran 5 ga wata cewa, an gano abin tiriri na Cesium a jikin nau’in kifin da aka kama a gulf din tashar nukiliya ta Fukushima, yawansa ya ninka sau 180 bisa na ma’aunin da aka tanada.

A sa’i daya kuma, igiyar ruwa a wannan wuri na da karfi matuka, matakin da ya sa idan an zuba ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, zai yadu zuwa duk fadin tekun duniya a cikin shekaru 10 masu zuwa, abin da zai kawo babbar illa ga muhallin teku da lafiyar jikin Bil Adama.

Labarai Masu Nasaba

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Bisa dokar kasa da kasa, ruwan dagwalon nukiliya na Fukushima shara ce, dole ne a ajiye su a maimakon zuba su a cikin teku. Misali a tashar samar da wutar lantarki ta amfani da karfin nukiliya ta kasar Faransa, an kafa cibiyar adana sharar da tashar ke samarwa, matakin da ya fi dacewa.

Gwamnatin Japan ta fitar da shirye-shirye da dama game da yadda za a yi da ruwan dagwalon nukiliya na tashar Fukushima tun daga shekarar 2013, amma daga karshe ta zabi wannan shiri maras imani don yin tsimin kudi da kare kanta.

Shin ko gwamnatin Japan ba ta da isashen kudi? A’a, ba ta da imani ne! Matakin ta zai kawowa muhalli matukar barazana, har ma ya illata makomar Bil Adama baki daya. (Mai zana da rubuta: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Amurka Ba Za Su Iya Dakatar Da Matakan Sulhu Na Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Next Post

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Related

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

1 hour ago
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

3 hours ago
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
Daga Birnin Sin

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

3 hours ago
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
Daga Birnin Sin

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

5 hours ago
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
Daga Birnin Sin

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

7 hours ago
Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira

8 hours ago
Next Post
Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai - Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.