• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Hajjin Bana

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukaci maniyyatan jihar zuwa Saudiyya su kasance masu biyayya da bin doka da oda, kuma su kasance jakadu na gari ga jihar da Nijeriya a yayin da suke ƙkasa mai tsarki. 

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a jiya yayin jawabin sa na bankwana ga maniyyatan jihar a hukumar jin dadin alhazai ta Jihar Gombe, “Yayin da kuke kasa mai tsarki, don Allah ku kasance jakadu nagari ga kanku, da al’ummarku, da kananan hukumominku, da Jihar Gombe dama Nijeriya, don mu yi alfahari da ku,” in ji shi.

  • Hajjin Bana: Kashin Farko Na Maniyyatan Adamawa 475 Sun Sauka Saudiyya

Da yake kira ga maniyyatan su nesanta kansu daga duk wani abu da ka iya bata musu aikin na Hajji, ko taba mutuncin su ko na Jihar Gombe, Gwamna Inuwa ya tunatar da su cewa a kasa mai tsarki doka tana aiki ba sani ba sabo kan duk wadda aka kama da aikata laifi ko rashin gaskiya.

 

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

Da yake yi wa maniyyatan fatan gudanar da karbabben aikin Hajji, gwamnan ya karfafa su da su rika tambayar jagororinsu kan duk wani abu da ya shige mu su duhu. Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen ganin alhazan jihar sun yi aikin Hajji cikin natsuwa tun daga Nijeriya har zuwa kasa mai tsarki.

Hajjin Bana

Da yake tsokaci kan matsalolin rayuwa dana tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci maniyatan su zage damtse wajen yin addu’o’in Allah ya samar wa kasar mafita.

 

Gwamnan ya kuma bukaci jami’an hukumomin alhazai a dukkan matakai su gudanar da ayyukan su cikin gaskiya da amana da kishin kasa don gudanar da aikin Hajjin cikin nasara.

 

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe, Mai Martaba Sarkin Dukku, Haruna Abdulkadir Rasheed, ya yaba wa gwamnan bisa jajircewarsa na ganin an gudanar da aikin Hajji na bana cikin nasara.

 

Da yake jan hankalin alhazan jihar su maida hankali ga ibada maimakon sayen tsaraba, shugaban ya bukaci maniyyatan su ba da hadin kai ga jami’an aikin Hajji na jiha da na kasa don samun nasarar gudanar da aikin.

Hajjin Bana

A jawabinsa na maraba, babban sakataren hukumar Alhaji Sa’adu Hassan, ya yaba wa gwamnan bisa samar da ingantaccen masauki ga maniyyatan jihar a ƙasa mai tsarki.

 

Ya ce da farko jirgi mai daukar alhazai 350 aka tsara zai yi jigilar alhazan jihar, amma bisa jajircewar da gwamnan ya yi, yanzu an samar da jirgi mai daukan mutum 550 da zai tashi da sawun farko na maniyyatan jihar. Ya ce bayan tantance maniyyatan da aka lika sunayensu, za a fara jigilar mahajjatan gadan-gadan a gobe Laraba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version