• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Jaje Tsafe, Ya Nanata Muradin Magance Matsalar Tsaro

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Jaje Tsafe, Ya Nanata Muradin Magance Matsalar Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a yau Alhamis ya tabbatar da aniyar gwamnatinsa na magance matsalar tsaron da ke addabar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ziyarar jajantawa da ya kai fadar Sarkin Tsafe, Alhaji Muhammadu Bawa bisa harin rashin imanin da ‘yan bindiga suka kai garin.

Wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce Gwamnan ya je Tsafe ne don ya yi jaje, ya kuma tabbatarwa jama’a Æ™udurinsa na yi wa tufkar hanci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana 12 Ga Watan Yuni, Ranar Hutu

 

Gwamnan ya bayyana damuwarsa kan hare-haren da aka samu a wasu yankuna ciki har da Tsafe.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

“Na kawo wannan ziyara ne domin jajantawa masarauta da al’ummar Æ™aramar hukumar Tsafe bisa harin da ‘yan bindiga suka kai musu.

“Ina so na tabbatarwa da mai martaba da al’ummarmu cewa tsaro shi ne abu mafi muhimmanci ga gwamnatinmu, dalilin da ya sa nake aiki da sauran É“angarorin tsaro don tabbatar da wanzuwar zaman lafiya.

“Ni da wasu gwamnoni mun samu damar ganawa da Shugaban Ƙasa Tinubu a Abuja, kuma na bijiro mishi da maganar rashin tsaro a Zamfara. Shugaban Æ™asan ya tabbatar da zai bani cikakken goyon baya. Don haka ne ma na sake neman alfarmar sake zaunawa da shi don mu tattauna wannan matsalar.

“Lokacin da aka sanar da ni labarin wannan hari na ‘yan bindiga a Tsafe, a take na kira jami’an tsaro, inda suka kai É—aukin gaggawa.

“Yayin da gwamnati ke aiki don magance wannan matsala, ina kira ga al’umman Jihar Zamfara da su Æ™arfafa yin addu’a ga wannan jiha. Muna matuÆ™ar buÆ™atar goyon baya a wannan al’amari.”

Sarkin Tsafe, Alhaji Muhammadu Bawa, a nashi jawabin, ya roki Allah Ya yi jagora ga Gwamna Lawal, musamman la’akari da irin jajircewarshi don ganin an samu zaman lafiya a Zamfara.

“Ina so na yi godiya tare da jinjina ga Gwamna bisa wannan ziyarar jaje da ya kawo mana. Ba zan iya É“oye farin cikina ba, saboda wannan shi ne karo na farko da aka samu Gwamna ya tako don jajanta mana kan harin ‘yan bindiga.

“Haka nan kuma dole ne na jinjinawa irin taimakon gaggawa da muka samu daga Gwamna, wanda ya dakile yiwuwar dawowar ‘yan bindigan. Za mu ba wannan sabuwar gwamnati duk wata gudummawa da take buÆ™ata a wannan shiri nata na kawo Æ™arshen matsalar Zamfara”, in ji Sarkin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Sin Zai Ci Gaba Da Zama Injin Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

40 minutes ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

1 hour ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

3 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

8 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

9 hours ago
Next Post
Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.