• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Jaje Tsafe, Ya Nanata Muradin Magance Matsalar Tsaro

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Jaje Tsafe, Ya Nanata Muradin Magance Matsalar Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a yau Alhamis ya tabbatar da aniyar gwamnatinsa na magance matsalar tsaron da ke addabar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ziyarar jajantawa da ya kai fadar Sarkin Tsafe, Alhaji Muhammadu Bawa bisa harin rashin imanin da ‘yan bindiga suka kai garin.

Wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce Gwamnan ya je Tsafe ne don ya yi jaje, ya kuma tabbatarwa jama’a Æ™udurinsa na yi wa tufkar hanci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana 12 Ga Watan Yuni, Ranar Hutu

 

Gwamnan ya bayyana damuwarsa kan hare-haren da aka samu a wasu yankuna ciki har da Tsafe.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

“Na kawo wannan ziyara ne domin jajantawa masarauta da al’ummar Æ™aramar hukumar Tsafe bisa harin da ‘yan bindiga suka kai musu.

“Ina so na tabbatarwa da mai martaba da al’ummarmu cewa tsaro shi ne abu mafi muhimmanci ga gwamnatinmu, dalilin da ya sa nake aiki da sauran É“angarorin tsaro don tabbatar da wanzuwar zaman lafiya.

“Ni da wasu gwamnoni mun samu damar ganawa da Shugaban Ƙasa Tinubu a Abuja, kuma na bijiro mishi da maganar rashin tsaro a Zamfara. Shugaban Æ™asan ya tabbatar da zai bani cikakken goyon baya. Don haka ne ma na sake neman alfarmar sake zaunawa da shi don mu tattauna wannan matsalar.

“Lokacin da aka sanar da ni labarin wannan hari na ‘yan bindiga a Tsafe, a take na kira jami’an tsaro, inda suka kai É—aukin gaggawa.

“Yayin da gwamnati ke aiki don magance wannan matsala, ina kira ga al’umman Jihar Zamfara da su Æ™arfafa yin addu’a ga wannan jiha. Muna matuÆ™ar buÆ™atar goyon baya a wannan al’amari.”

Sarkin Tsafe, Alhaji Muhammadu Bawa, a nashi jawabin, ya roki Allah Ya yi jagora ga Gwamna Lawal, musamman la’akari da irin jajircewarshi don ganin an samu zaman lafiya a Zamfara.

“Ina so na yi godiya tare da jinjina ga Gwamna bisa wannan ziyarar jaje da ya kawo mana. Ba zan iya É“oye farin cikina ba, saboda wannan shi ne karo na farko da aka samu Gwamna ya tako don jajanta mana kan harin ‘yan bindiga.

“Haka nan kuma dole ne na jinjinawa irin taimakon gaggawa da muka samu daga Gwamna, wanda ya dakile yiwuwar dawowar ‘yan bindigan. Za mu ba wannan sabuwar gwamnati duk wata gudummawa da take buÆ™ata a wannan shiri nata na kawo Æ™arshen matsalar Zamfara”, in ji Sarkin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Sin Zai Ci Gaba Da Zama Injin Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

2 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

3 hours ago
zamfara
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

4 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

6 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

6 hours ago
zamfara
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

9 hours ago
Next Post
Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
zamfara

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.