• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban sakataren kungiyar masu sarrafa Takin zamani da rabar da shi  na kasa FEPSAN Mista  Gideon Nagedu ya bukaci  shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu da ya yi bincike akan masana’antar samar  da Takin zamani kan yadda ta kasance a shekaru bakwai da suka gabata.

Nagedu a wata hirarsa da manema labarai ya bayyana cewa, abinda muka bukata daga gun gwamnatin shugaba Tinibu shine ya yi bincike akan masana’antar samar  da Takin zamani kan yadda ta kasance a shekaru bakwai da suka gabata.

  • Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya
  • Zan Yi Aiki A Bayyane Tare Da Shugabannin Majalisa Ta 10 – Tinubu

Sai dai, sakataren ya yi nuni da cewa, idan zamu yiwa tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari adalci, gwamnatin ta samar da gagaruwar ci gaba wajen habaka fannin samar da Takin zamani a kasar nan

Ya ci daga da cewa, a lokacin tsohuwar gwamnatin ta Buhari, an samar da Takin zamani da ya karu zuwa tan miliyan 1.6 wanda wannan ne ya kasance na karon farko a kasar nan.

“An samar da Takin zamani da ya karu zuwa tan miliyan 1.6 wanda wannan ne ya kasance na karon farko a kasar nan a lokacin tsohuwar gwamnatin Buhari.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Nagedu ya kara da cewa, za ka iya gani da Idonka a karkashin shirin samarr da Takin zamani na fadar shugban kasa a lokacin tsohuwar gwamnatin ta Buhari, an samar da ci gaba matuka.

A cewarsa, a kungiyance, duk irin nasarar da tsohuwar gwamnatin ta Buhari ta samar a fannin aikin noma a kasar nan, muna kira ga shugaba Tinibu da ya dora kan sanar da gwamnatin baya ta samar a fannin.

“Duk irin nasarar da tsohuwar gwamnatin ta Buhari ta samar a fannin aikin noma a kasar nan, muna kira ga shugaba Tinibu da ya dora kan sanar da gwamnatin baya ta samar a fannin.”

Daya bangaren da muka bukatar gwamnatin ta Tinubu ta mayar da hankaili akai Sakataren ya sanar da cewa, muna kira ga Tinubu da ya mayar da hankali wajn bunkasa samar da kudaden musaya na ketare, inda hakan zai kara bai wa habaka fannin na aikin noma.

Ya bayyana cewa, daya bangaren da muka bukatar Tinubu ya mayar da hankali akai shine magance yadda wasu masu sarrafa Takin zamani ke gurbata shi, inda hakan ke janyo wa masu zuba jari a fannin da kuma manoma asara.

A cewarsa, matukara gwamnatin ta kawo karshen wannan matsalar, manoman kasar nan za su samu sukunin yin girbe amfanin gonakan su mai yawa.

“Muna bukatar shugaban kasa Tinubu ya mayar da hankali akai shi ne magance yadda wasu masu sarrafa Takin zamani ke gurbata shi, inda hakan ke janyo wa masu zuba jari a fannin da kuma manoma asara.”

A wani labarain kuwa, Manoman Albasa sunce sun yi asarar sama da Naira biliyan uku a duka shekara saboda rashin sarrafa ta yadda ya dace a cikin kasar nan.

Shugaban kungiyar manoman Albasa da sararrafa ta na kasa Isah Aliyu ya bayyana hakan, inda ya ce, Nijeriya  na noma Albasa metric tan miliyan biyu na Albasa a duk shekara.inda hakan ya kai kimanin kashi 40 a cikin dari na jimlar Alabsar da ake nomawa a kasar.

“Nijeriya na noma Albasa metric tan miliyan biyu na Albasa a duk shekara.inda hakan ya kai kimanin kashi 40 a cikin dari na jimlar Alabsar da ake nomawa a kasar. “

Aliyu wanda ya sanar da hakan a taron kaddamar da kamfanin sarrafa Albasa da Tafarnuwa wanda ya kasance irinsa na farko a jihar Sokoto ya ci gaba da cewa, duk da cewa Nijeriya ta kasance kan gaba wajen noman Albasa da Tafarnuwa a duniya, amma ta kasance tana shigo da amfanin cikin kasar nan saboda rashin kayan da za a sarrafa wadannan amfanin biyu.

“Kasance irinsa na farko a jihar Sokoto ya ci gaba da cewa, duk da cewa Nijeriya ta kasance kan gaba wajen noman Albasa da Tafarnuwa a duniya,  amma ta kasance tana shigo da amfanin cikin kasar nan saboda rashin kayan da za a sarrafa wadannan amfanin biyu.”

Shugaban ya kara da cewa, rashin kayan da za sarrafa amfanin biyu a kasar nan, na ci gaba da zamowa manoman da ke noma su, babban tarnaki.

A cewarsa,”Sama da metric tan miliyan biyu 2 na Albasa ake nomawa a kasar nan a duk shekara,  inda jihar Sokoto ke noma kashi 40 a cikin dari.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KumngiyaManomaTakiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

Next Post

Abin Da Ya Sa Manoman Katsina Suka Mayar Da Martani Kan Alkwarin Gwamna Radda

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

4 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

4 weeks ago
Next Post
Abin Da Ya Sa Manoman Katsina Suka Mayar Da Martani Kan Alkwarin Gwamna Radda

Abin Da Ya Sa Manoman Katsina Suka Mayar Da Martani Kan Alkwarin Gwamna Radda

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.