ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar

by Abubakar Abba
3 years ago
Taki

Babban sakataren kungiyar masu sarrafa Takin zamani da rabar da shi  na kasa FEPSAN Mista  Gideon Nagedu ya bukaci  shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu da ya yi bincike akan masana’antar samar  da Takin zamani kan yadda ta kasance a shekaru bakwai da suka gabata.

Nagedu a wata hirarsa da manema labarai ya bayyana cewa, abinda muka bukata daga gun gwamnatin shugaba Tinibu shine ya yi bincike akan masana’antar samar  da Takin zamani kan yadda ta kasance a shekaru bakwai da suka gabata.

  • Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya
  • Zan Yi Aiki A Bayyane Tare Da Shugabannin Majalisa Ta 10 – Tinubu

Sai dai, sakataren ya yi nuni da cewa, idan zamu yiwa tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari adalci, gwamnatin ta samar da gagaruwar ci gaba wajen habaka fannin samar da Takin zamani a kasar nan

ADVERTISEMENT

Ya ci daga da cewa, a lokacin tsohuwar gwamnatin ta Buhari, an samar da Takin zamani da ya karu zuwa tan miliyan 1.6 wanda wannan ne ya kasance na karon farko a kasar nan.

“An samar da Takin zamani da ya karu zuwa tan miliyan 1.6 wanda wannan ne ya kasance na karon farko a kasar nan a lokacin tsohuwar gwamnatin Buhari.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Nagedu ya kara da cewa, za ka iya gani da Idonka a karkashin shirin samarr da Takin zamani na fadar shugban kasa a lokacin tsohuwar gwamnatin ta Buhari, an samar da ci gaba matuka.

A cewarsa, a kungiyance, duk irin nasarar da tsohuwar gwamnatin ta Buhari ta samar a fannin aikin noma a kasar nan, muna kira ga shugaba Tinibu da ya dora kan sanar da gwamnatin baya ta samar a fannin.

“Duk irin nasarar da tsohuwar gwamnatin ta Buhari ta samar a fannin aikin noma a kasar nan, muna kira ga shugaba Tinibu da ya dora kan sanar da gwamnatin baya ta samar a fannin.”

Daya bangaren da muka bukatar gwamnatin ta Tinubu ta mayar da hankaili akai Sakataren ya sanar da cewa, muna kira ga Tinubu da ya mayar da hankali wajn bunkasa samar da kudaden musaya na ketare, inda hakan zai kara bai wa habaka fannin na aikin noma.

Ya bayyana cewa, daya bangaren da muka bukatar Tinubu ya mayar da hankali akai shine magance yadda wasu masu sarrafa Takin zamani ke gurbata shi, inda hakan ke janyo wa masu zuba jari a fannin da kuma manoma asara.

A cewarsa, matukara gwamnatin ta kawo karshen wannan matsalar, manoman kasar nan za su samu sukunin yin girbe amfanin gonakan su mai yawa.

“Muna bukatar shugaban kasa Tinubu ya mayar da hankali akai shi ne magance yadda wasu masu sarrafa Takin zamani ke gurbata shi, inda hakan ke janyo wa masu zuba jari a fannin da kuma manoma asara.”

A wani labarain kuwa, Manoman Albasa sunce sun yi asarar sama da Naira biliyan uku a duka shekara saboda rashin sarrafa ta yadda ya dace a cikin kasar nan.

Shugaban kungiyar manoman Albasa da sararrafa ta na kasa Isah Aliyu ya bayyana hakan, inda ya ce, Nijeriya  na noma Albasa metric tan miliyan biyu na Albasa a duk shekara.inda hakan ya kai kimanin kashi 40 a cikin dari na jimlar Alabsar da ake nomawa a kasar.

“Nijeriya na noma Albasa metric tan miliyan biyu na Albasa a duk shekara.inda hakan ya kai kimanin kashi 40 a cikin dari na jimlar Alabsar da ake nomawa a kasar. “

Aliyu wanda ya sanar da hakan a taron kaddamar da kamfanin sarrafa Albasa da Tafarnuwa wanda ya kasance irinsa na farko a jihar Sokoto ya ci gaba da cewa, duk da cewa Nijeriya ta kasance kan gaba wajen noman Albasa da Tafarnuwa a duniya, amma ta kasance tana shigo da amfanin cikin kasar nan saboda rashin kayan da za a sarrafa wadannan amfanin biyu.

“Kasance irinsa na farko a jihar Sokoto ya ci gaba da cewa, duk da cewa Nijeriya ta kasance kan gaba wajen noman Albasa da Tafarnuwa a duniya,  amma ta kasance tana shigo da amfanin cikin kasar nan saboda rashin kayan da za a sarrafa wadannan amfanin biyu.”

Shugaban ya kara da cewa, rashin kayan da za sarrafa amfanin biyu a kasar nan, na ci gaba da zamowa manoman da ke noma su, babban tarnaki.

A cewarsa,”Sama da metric tan miliyan biyu 2 na Albasa ake nomawa a kasar nan a duk shekara,  inda jihar Sokoto ke noma kashi 40 a cikin dari.”

Taki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Manoman Katsina Suka Mayar Da Martani Kan Alkwarin Gwamna Radda

Abin Da Ya Sa Manoman Katsina Suka Mayar Da Martani Kan Alkwarin Gwamna Radda

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.