• English
  • Business News
Monday, May 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsari Ne Babba Sakin Nnamdi Kanu —Asari Dokubo

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Hatsari Ne Babba Sakin Nnamdi Kanu —Asari Dokubo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jagora a yankin Niger Delta, Asari Dokubo, ya bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da kada ya saki shugaban haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu.

Dokubo wanda ke tattauna da ‘yan jarida bayan wata ganawa da ya yi da shugaban kasa a fadar shugaban kasa da ke Villa Abuja ranar Juma’a.

  • Kungiyoyin Arewa Sun Yi Fatali Da Bukatar Sakin Nnamdi Kanu
  • Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi

Jagoran Niger Delta, ya ce, sakin Kanu tamkar farfado ayyukan ci gaba da kashe mutane da aikace-aikacen ta’addanci ne, kuma hakan zai zama tamkar tukuici ne ga laifukan da ya aikata, ya ce, kamatuwa ya yi Kanu ya fuskanci shari’a.

Idan za a tuna, tun lokacin da aka sake kama Kanu a 2021 yake tsare a hannun hukumar DSS inda ke fuskantar shari’ar zargin ta’addanci.

A shekarar 2017 ne kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da belin Kanu amma ya karya ka’idojin belinsa lamarin da ya sanya shi arcewa daga Nijeriya zuwa kasar waje, sannu a hankali kuma jami’an tsaro suka sake kamo shi.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya sha matsin lamba na bukatar ya sake Kanu amma ya yi mursisi, inda a yanzu bayan kafa sabuwar gwamnati wasu da dama suke ta sabunta kiran a sake shugaban na IPOB.

Da yake magana kan tsare Kanu, Asari Dokubo ya ce, “Sakin Nnamdi Kanu tamkar biyan tukuici ne ga ayyukan ta’addanci da kisan rayukan wadanda ba su ji ba su gani ba.”

Ya kara da cewa, “Kamatuwa ya yi kawai ya fuskanci shari’a kan ayyukansa da laifukan da ya aikata.” Cewar Dokubo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Asiri DokuboNnamdi Kanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Dubban Matasa Tare Da Sace Shanu A Jihar Neja

Next Post

Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

Related

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2
Tsaro

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

3 hours ago
Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake
Labarai

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

6 hours ago
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota
Labarai

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

7 hours ago
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa
Labarai

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

9 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Labarai

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

11 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

11 hours ago
Next Post
Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

May 25, 2025
Fasahar Shayi Ta Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankali Da Nishadi Ga ‘Yan Nijeriya

Fasahar Shayi Ta Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankali Da Nishadi Ga ‘Yan Nijeriya

May 25, 2025
Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

May 25, 2025
Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

May 25, 2025
Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

May 25, 2025
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

May 25, 2025
Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

May 25, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

May 25, 2025
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

May 25, 2025
An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

May 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.