• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Inuwar gamayyar masu ruwa da tsaki a kan ilimi a Jihar Kano sun nuna goyon bayansu na kwato muhallan makarantu da gwamnatin mai ci yanzu ta ke yi.

Dakta Ibrahim Usman Aikawa ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da suka gudanar a ranar Talata.

  • An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato
  • Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Ya ce taron nasu na wayarwa da mutane kai ne, a kan martabar da darajar ilimi da nuna goyon baya ga matakai da gwamnati a Jihar Kano ta dauka a kan filayen makarantu da ake karbowa.

Ya yi nuni da cewa suna sane da cewa wasu za su samu rashin jindadi a kan abin da yake faruwa amma wannan abu an yi shi ne don ci gaban al’umma domin magabata sun san martaba na ilimin Addinin dana boko saboda daraja da girmama ilimi Manzon Allah ya yi umarni aje a nemi ilimi ko a birnin Sin ne.

Dakta Aikawa, ya ce “marigayi Nelson Mandela na Afirka ta Kudu, ya ce ilimi ne makami da za ka yi amfani da shi da za ka iya juya duniya ta abin da kake so, amma a wannan yanayin ne aka samu wasu marasa kishi da rashin kaunar ci gaban ilimi a Kano suka handame filayen makarantu suka mayar da su gidaje da shaguna da wajen taron biki da wasanni.”

Labarai Masu Nasaba

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Ya ce duk wanda ya yi korafi a kan an rushe masa gida cewa yake a filin Salanta, ba sa cewa a filin makarantar Kano Poly saboda sanin idan suka fadi haka kowa zai gane sun shiga harkar filin ne.

Ya ce akwai wanda ya ce ya kashe miliyan 800 a gininsa duk wanda zai iya kashe irin wannan kudi ya gina gida da wuya a samu iyalansa na zuwa makarantun gwamnati sai wanda zai biya ko ba a kasar nan ba su yi karatu, amma ya zo ya debi kayan talakawa ya yi gini a kai saboda ana so a mallake ‘yancin talaka a hana ‘ya’yansu ilimi.

Aikawa, ya yi kira ga Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf a kan ya ci gaba da daukar matakai irin wadannan na rushe gini da aka yi ba bisa ka’ida ba, a kan zalunci don rusa ilimi a Jihar Kano.

Ya kara da cewa ya kamata a dauki tsauraran matakai na yin dokoki don hana wani nan gaba ya sake sayar da wajen makarantu na al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGamayyar Masu Ruwa TsakikanoRusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato

Next Post

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i

Related

Kano
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

53 minutes ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

2 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

3 hours ago
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

13 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

15 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

17 hours ago
Next Post
EFCC Ta Tsare Tsohon Gwamnan Benuwe, Ortom

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa'o'i

LABARAI MASU NASABA

Kano

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.