ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato

by Sadiq
3 years ago
Filato

Akalla mutane 15 ne aka tabbatar da mutuwarsu a wasu sabbin hare-hare da aka kai a kauyukan Bwai da Chisu na karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.

LEADERSHIP ta tattaro cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Talata lokacin da mazauna garin suka kwanta barci.

  • Aiwatar Da Alkawain Da Aka Yi Yana Da Muhimmanci
  • Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Bincike ya nuna cewa maharan sun afkawa al’ummomin biyu lokaci guda inda suka kashe mutane tare da kone gidaje.

ADVERTISEMENT

Wani shaidan gani da ido, Bamshak Ishaya ya yi zargin cewa ‘yan bindigar Fulani ne suka kashe wasu mutane a gidan wani shugaban al’umma a kauyen Chisu a daren ranar Talata da misalin karfe 11:00 na dare.

An gano cewa an kuma kone Cocin COCIN RCC da ke Bwai da ke kan hanyar Mangu zuwa Bokkos tare da kone gidaje da motoci da babura masu kafa uku.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Wakilinmu ya ruwaito cewa, al’ummar yankin sun ji karar harbe-harbe, inda suka garzaya zuwa gidan Jagoran unguwarsu, don neman mafaka.

A Bwai, baya ga Cocin, an kuma kone gidaje da ke kusa da kasuwar, sannan an kone wata mata a yankin.

A halin da ake ciki, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Mangu ta kudu a majalisar dokokin jihar, Mista Bala Fwangje shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce, “da misalin karfe 11 na dare, mun samu waya cewa makiyaya sun shigo Chisu da Bwai, da safiyar yau ne muka ji an kashe kimanin mutane 15, an lalata gidaje, an kone dukiyoyi da dama, har yanzu ban samu cikakken bayani ba.”

Haka zalika, shugaban kwamitin riko na karamar hukumar Mangu, Mista Markus Artu, ya shaida wa manema labarai ta wayar tarho cewa lamarin ya faru amma har yanzu ba shi da cikakken bayani.

Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Filato, DSP Afred Alabo ba mu samu jin ta bakinsa ba har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Filato
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Filato

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Filato

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.