• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
Tattalin arziki

Yau Alhamis 29 ga wata ne, aka kaddamar da bikin baje-kolin tattalin arziki da cinikayya na kasashen Sin da Afirka karo na uku a birnin Changsha na lardin Hunan na kasar Sin, wato China-Africa Economic and Trade EXPO. Ana sa ran cewa, bikin na bana zai kara taka muhimmiyar rawa, da baje karin hajojin Sin da Afirka, al’amarin da zai sanya sabon kuzari ga hadin-gwiwar bangarorin biyu.

Yawan kamfanonin cikin gida da waje da suke halartar bikin na bana, ya kai 1500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari idan aka kwatanta da bikin da ya gabata. Kana, kayayyaki 1590 daga kasashe 29 ne, aka yi rajistar shigar da su baje-koli na bana. Ana kuma shirin rattaba hannu ko kuma gudanar da shawarwari kan wasu ayyukan hadin-gwiwa guda 218, wadanda jimillar darajarsu ta kai dala biliyan 19.1.

  • Sin Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwarta Da Afrika

A bana ne ake cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kasar Sin ta yi, kana shekaru 10 da kasar ta fitar da muhimman manufofinta kan nahiyar Afirka, wato nuna “Sahihanci”, da “Sakamako na hakika”, da “Dangantakar abokantaka”, da kuma “Aminci”. A cikin wadannan shekaru 10, kwalliya ta biya kudin sabulu, wajen karfafa hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da kasuwanci.

Bikin baje-kolin tattalin arziki da cinikayyar Sin da Afirka, dandalin hadin-gwiwa ne mafi girma a karkashin tsarin FOCAC, wato dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka. Tun daga shekara ta 2019, a kan shirya irin wannan biki bayan kowane shekaru biyu-biyu. A ranar 2 ga watan Yuli ne, za a kammala bikin na bana.

Sannan, a yau Alhamis, babbar hukumar kwastan ta kasar Sin ta gabatar da alkaluman cinikayya tsakanin Sin da Afrika karon farko yayin bikin baje kolin harkokin cinikayya na Sin da Afrika karo na 3. Bisa alkaluman, makin cinikayya a shekarar 2000 ya kai 100, yayin da a shekarar 2022 ya karu zuwa maki 990.55, abin da ya bayyana saurin bunkasuwar cinikayyar bangarorin biyu. A cikin wadannan shekaru kuma, yawan kudin dake shafar cinikin kayayyakin da Sin ke fitarwa zuwa Afrika ya ninka fiye da sau 20, wanda ya karu da kashi 17.7 a ko wace shekara. Hakan ya sa Sin ta kai matsayin koli a fannin ciniki da Afrika a cikin shekaru 14 a jere.

LABARAI MASU NASABA

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

A wannan rana kuma, an bude dandalin hadin kai a fannin kiwo lafiyar bil Adama da tsirrai tsakanin Sin da Afrika wato SPS a birnin Changsha, hedkwatar lardin Hunan. Yayin dandalin, wakilin babbar hukumar kwastan ya yi bayani kan nagartattun matakai da za su tabbatar da kafa hanyar samar da rangwame ga kayayyakin aikin gona da Sin za ta shigo da su daga Afrika. (Murtala Zhang, Amina Xu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Next Post
Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

LABARAI MASU NASABA

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.