ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

by CMG Hausa
3 years ago
Tattalin arziki

Yau Alhamis 29 ga wata ne, aka kaddamar da bikin baje-kolin tattalin arziki da cinikayya na kasashen Sin da Afirka karo na uku a birnin Changsha na lardin Hunan na kasar Sin, wato China-Africa Economic and Trade EXPO. Ana sa ran cewa, bikin na bana zai kara taka muhimmiyar rawa, da baje karin hajojin Sin da Afirka, al’amarin da zai sanya sabon kuzari ga hadin-gwiwar bangarorin biyu.

Yawan kamfanonin cikin gida da waje da suke halartar bikin na bana, ya kai 1500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari idan aka kwatanta da bikin da ya gabata. Kana, kayayyaki 1590 daga kasashe 29 ne, aka yi rajistar shigar da su baje-koli na bana. Ana kuma shirin rattaba hannu ko kuma gudanar da shawarwari kan wasu ayyukan hadin-gwiwa guda 218, wadanda jimillar darajarsu ta kai dala biliyan 19.1.

  • Sin Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwarta Da Afrika

A bana ne ake cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kasar Sin ta yi, kana shekaru 10 da kasar ta fitar da muhimman manufofinta kan nahiyar Afirka, wato nuna “Sahihanci”, da “Sakamako na hakika”, da “Dangantakar abokantaka”, da kuma “Aminci”. A cikin wadannan shekaru 10, kwalliya ta biya kudin sabulu, wajen karfafa hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Bikin baje-kolin tattalin arziki da cinikayyar Sin da Afirka, dandalin hadin-gwiwa ne mafi girma a karkashin tsarin FOCAC, wato dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka. Tun daga shekara ta 2019, a kan shirya irin wannan biki bayan kowane shekaru biyu-biyu. A ranar 2 ga watan Yuli ne, za a kammala bikin na bana.

Sannan, a yau Alhamis, babbar hukumar kwastan ta kasar Sin ta gabatar da alkaluman cinikayya tsakanin Sin da Afrika karon farko yayin bikin baje kolin harkokin cinikayya na Sin da Afrika karo na 3. Bisa alkaluman, makin cinikayya a shekarar 2000 ya kai 100, yayin da a shekarar 2022 ya karu zuwa maki 990.55, abin da ya bayyana saurin bunkasuwar cinikayyar bangarorin biyu. A cikin wadannan shekaru kuma, yawan kudin dake shafar cinikin kayayyakin da Sin ke fitarwa zuwa Afrika ya ninka fiye da sau 20, wanda ya karu da kashi 17.7 a ko wace shekara. Hakan ya sa Sin ta kai matsayin koli a fannin ciniki da Afrika a cikin shekaru 14 a jere.

LABARAI MASU NASABA

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”

A wannan rana kuma, an bude dandalin hadin kai a fannin kiwo lafiyar bil Adama da tsirrai tsakanin Sin da Afrika wato SPS a birnin Changsha, hedkwatar lardin Hunan. Yayin dandalin, wakilin babbar hukumar kwastan ya yi bayani kan nagartattun matakai da za su tabbatar da kafa hanyar samar da rangwame ga kayayyakin aikin gona da Sin za ta shigo da su daga Afrika. (Murtala Zhang, Amina Xu)

Tattalin arziki
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
Daga Birnin Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”

September 13, 2026
Xi Ya Halarci Taron BRICS A New Delhi
Daga Birnin Sin

Xi Ya Halarci Taron BRICS A New Delhi

September 12, 2026
Next Post
Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

LABARAI MASU NASABA

Tattalin arziki

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Tattalin arziki

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
Yajin Aikin ASUU: Malaman Jami’ar Jihar Kaduna Sun Bijirewa El-rufa’i

Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

September 13, 2026
Gwamna Fintiri, Dangote Da Sarakunan Gargajiya Sun Halarci Jana’izar Bamanga Tukur A Yola

Gwamna Fintiri, Dangote Da Sarakunan Gargajiya Sun Halarci Jana’izar Bamanga Tukur A Yola

September 13, 2026
Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”

Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”

September 13, 2026
Tsohon Kwamishina A Gombe, Ya Marawa Pantami Baya

Tsohon Kwamishina A Gombe, Ya Marawa Pantami Baya

September 13, 2026
Doma United Na Cigaba Da Jan Zarenta A Firimiyar Nijeriya Bayan Doke Enyimba

Doma United Na Cigaba Da Jan Zarenta A Firimiyar Nijeriya Bayan Doke Enyimba

September 13, 2026
Hafsat Bakari Ta Sake Dawo Da Sarƙaƙƙen Al’amari

Hafsat Bakari Ta Sake Dawo Da Sarƙaƙƙen Al’amari

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.