• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

by CMG Hausa
2 years ago
Xi Jinping

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci taro na 23 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin-kai ta Shanghai ko kuma SCO a takaice, da maraicen yau Talata 4 ga wata a Beijing, inda ya gabatar da muhimmin jawabi.

A jawabin nasa, Xi ya nuna cewa, a halin yanzu duniyar mu tana fuskantar rikice-rikice da yawa, kana, dan Adam na fuskantar kalubalen da ba’a taba ganin irinsa ba.

  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Musaya Da Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

Tambaya a nan ita ce, hadin-gwiwa ko rarrabuwar kawuna, zaman lafiya ko rikice-rikice, zaman tsintsiya madaurinki daya ko zaman fito-na-fito, wane ake bukata? Amsa ta ita ce, fatan al’ummun kasa da kasa game da more rayuwa mai dadi, shi ne babban aikin dake gaban mu, kana kuma, babu wani mutum ko wata kasa, da za ta iya hana ayyukan wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da inganta hadin-gwiwa, da neman cimma moriya tare a duniyar mu.

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa, kasar sa na fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, don aiwatar da shawarar tabbatar da tsaro a duk fadin duniya, da daidaita sabani tsakanin kasa da kasa ta hanyar yin shawarwari, da taimakawa wajen warware matsalolin kasa da kasa da na shiyya-shiyya ta hanyar siyasa.

Kaza lika kasar Sin tana kuma fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, wajen tabbatar da shawarar samar da ci gaban duk duniya, da tsayawa kan kokarin dunkule tattalin arzikin duniya na bai daya, da nuna adawa ga ra’ayin bada kariya, da sanya takunkumi a gefe daya, da ra’ayin nuna wariya da rarrabuwar kawuna, a wani kokari na kara samun nasarori don su amfani al’ummun kowace kasa bisa adalci. Kasar Sin tana maraba da bangarori daban-daban, da su aiwatar da shawarar inganta wayewar kai a duk fadin duniya, da nuna hakuri ga mabambantan al’adu, don kara samun fahimtar juna, da sada zumunta tsakanin jama’ar kasashe daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

A bana ne ake cika shekaru 10, tun bayan da kasar Sin ta bullo da shawarar “ziri daya da hanya daya”, inda za ta gudanar da babban dandalin tattaunawa na hadin-gwiwar kasa da kasa bisa shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3. Game da hakan, shugaba Xi ya ce, yana maraba da halartar bangarori daban-daban dandalin, ta yadda shawarar za ta kara samar da alfanu ga jama’ar duk fadin duniya. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
Next Post
Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.