• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Shafe Shekara 14 Ba A Biya Tsofaffin Ma’aikata Fansho Da Kudin Sallama A Adamawa Ba

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Aka Shafe Shekara 14 Ba A Biya Tsofaffin Ma’aikata Fansho Da Kudin Sallama A Adamawa Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Tsoffin Ma’aikata ta Kasa (NUP) a Jihar Adamawa, ta koka kan yadda aka kwashe shekara tara zuwa 14, ba tare da gwamnatin jihar ta biya tsofaffin ma’aikata kudin sallama ba.

Shugaban Kungiyar Tsofaffin Ma’aikata ta jihar, Muhammad Sali ne, ya bayyana haka ga manema labarai a Yola.

  • Hajji 2023: Alhazan Jihar Kwara 272 Sun Dawo Gida Nijeriya
  • Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje

Sali, ya ce shekaru da dama gwamnatin jihar ta gaza biyan tsofaffin ma’aikatan kudaden da su ke bi bashi.

Ya kara da cewa “Shekaru tara gwamnati ta gaza sallamar tsofaffin ma’aikatan jiha, shekara 14 ba ta biya kudaden sallamar tsofaffin ma’aikatan kananan hukumomin jihar ba, duk da alkawarin da mai girma gwamna ya yi mana,” in ji Sali.

Da yake magana game da kudaden fansho da gwamnatin ke biyan tsofaffin ma’aikatan duk wata, shugaban kungiyar yac e “da ban mamaki har yanzu mafi karancin fansho shi ne 4000, kana da shekaru 60, kana karbar dubu hudu ko kudin magani ba zai maka ba.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

“Gwamnatin jihar na biyan dubu 32 mafi karancin albashi, bisa doka dubu 25 za a biya a matsayin mafi karancin fansho a wata, amma mu har yanzu dubu hudu ake ba mu.

“Doka ne, ko an kara albashi ko ba a kara ba, duk shekara biyar ana kara kudin fansho, amma mu an kara albashin ba a kara mana ba, muna rokon mai girma gwamna da ya duba wannan batu.

“Kullum mambobin kungiyarmu mutuwa suke duk da akwai wa’adi, amma rashin samun yadda za a kula da kai da matsalolin rayuwa ke kashe da dama a cikinmu,” in ji Sali.

Kazalika, ya ce kungiyar mai mambobi dubu takwas a jihar, tun 2013 da aka biya su ba a sake biyan tsofaffin ma’aikatan kudaden sallama ba.

Don haka ya jaddada rokonsa ga gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, da ya yi wani abu domin ceto rayuwar tsofaffin ma’aikatan.

Haka kuma shugaban ya shawarci mambobin kungiyar da su ci gaba da hakuri zuwa lokacin da gwamnan zai share musu hawaye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaFanshoKudin SallamaKungiyar Tsofaffin Ma'aikata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajji 2023: Alhazan Jihar Kwara 272 Sun Dawo Gida Nijeriya

Next Post

Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

Related

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

1 hour ago
Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga
Labarai

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

2 hours ago
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu
Manyan Labarai

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

4 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

7 hours ago
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

18 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

20 hours ago
Next Post
Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

LABARAI MASU NASABA

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

July 13, 2025
Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

July 13, 2025
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.