• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Yi Wa Jama’a Kutse A Asusun Banki

byRabi'u Ali Indabawa
2 years ago
inKotu Da Ɗansanda
0
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Shelkwatar rundunar ‘yansanda ta Zone 2 da ke Onikan a Legas ta fatattaki wata kungiya da ta yi kutse a asusun kwastomomi na banki tare da damfarar su miliyoyin kudade.

Tuni dai an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu wajen zambar, yayin da ‘yansanda suka bayyana su a matsayin mambobin kungiyar.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku
  • Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

A wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yansandan shiyyar (ZPPRO) wadda ta kunshi jihohin Legas da Ogun, SP Hauwa Idris Adamu, ta fitar, ta ce ’yan kungiyar sun damfari mutum sama da 1000, wadanda suka watsu a fadin kasar nan.

Da take ba da bayanin yadda aka yi nasarar tarwatsa su, Adamu, ta ce, a ranar 8 ga Mayu, 2023, bankin United Bank for Africa (UBA) ya gabatar da koke ga Mataimakin Sufeto Janar na ‘yansanda, Mista Ari Ari Mohammed Ali, cewa akwai wasu kungiyoyin da suka kware kan zamba ta intanet na bankuna daban-daban a Nijeriya musamman United Bank for Africa (UBA), inda suka yi kutse cikin asusun kwastomomi tare da kwashe kudadensu.

“Bisa ga takardar koke, AIG ya tada wata tawagar ‘yansanda daga sashen sa ido na shiyyar, wadanda suka shiga aiki tare da taimakon fasahar zamani, mutum biyu da ake zargi; Yusuf Ademola mai shekaru 40 da Adesina Olawale Abiodun, 50, an gano su ne a maboyarsu da ke Ijebu Ode a Jihar Ogun.

 “Wadanda ake zargin sun amsa laifin da ake zargin su da aikatawa, kuma sun ce suna da kungiyoyi da dama a ko ina cikin fadin Nijeriya, wadanda suke amfani da manhajojin kwamfuta wajen yin kutse a cikin asusun abokan hulda da kuma fitar da kudadensu ba tare da an gano su daga bankin da suke so ba.

 “Duk da haka, tsarin da wadannan ‘yan damfara ke amfani da su shi ne samun lambar wayar abokin ciniki ta BBN da kuma sanarwar banki domin a samu saukin cire kudin.

Sakamakon haka, an yi kutse tare da zamba a asusun abokan ciniki sama da 1000 a duk fadin kasar nan. “Binciken da aka yi a kan lamarin ya nuna cewa an fito da ‘yan kungiyar ne daga sassa daban-daban na kasar nan, ana kuma kokarin kamo sauran wadanda ake zargi da hannu a wannan aika-aika.

“A cikin aiki na wucin gadi, ana ci gaba da bincike kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.”

Tags: 'YasandaAikaa-AikaKotu
ShareTweetSendShare
Rabi'u Ali Indabawa

Rabi'u Ali Indabawa

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

3 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

3 days ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

1 week ago
Next Post
Hanyoyin Magance Amosanin (Dandruff)

Hanyoyin Magance Amosanin (Dandruff)

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.