• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka sakatariyar baitulmalin kasar Amurka Janet Yellen na yin ziyarar aiki ta kwanaki hudu a kasar Sin, wadda kuma ta kasance ta biyu daga cikin manyan jami’an gwamnatin Biden da suka kawo ziyara a kasar Sin, biyo bayan ziyarar da sakataren harkokin wajen kasar Antony Blinken ya yi a watan da ya gabata. A labarin da aka bayar, an ce, da mista Antony Blinken da Madam Yellen dukkansu sun bayyana cewa, Amurka na son tabbatar da daidaiton da shugabannin kasashen biyu suka cimma a yayin ganawarsu a gefen taron kolin G20, wanda aka gudanar a bara a tsibirin Bali na kasar Indonesia, wato su martaba juna, da zama lafiya da juna, da kuma yi hadin gwiwa ta cin moriyar juna, kuma Amurka ba ta son ganin rarrabuwar kawuna a tsakaninta da kasar Sin. 

Amurka ta tura manyan jami’anta zuwa kasar Sin tare da yin kalaman da suka kasance tamkar neman kyautata hulda da kasar Sin, sai dai ba lallai al’amarin haka yake ba, kasancewar bayan da mista Blinken ya koma gida, ya bayyana wa ’yan jarida cewa, “sabanin dake tsakanin Sin da Amurka ba wani boyayyen abu ba ne. Kuma Amurka za ta ci gaba da kare moriyarta da akidunta, haka kuma za ta ci gaba da yin abin da kasar Sin ba ta son gani, tare da furta abubuwan da Sin din ba ta son ji.”

  • Ziyarar Xi Jinping A Jiangsu Na Da Nufin Inganta Aikin Gina Tsarin Masana’antu Na Zamani Na Kasar Sin

A hakika, sabanin da ke tsakanin Sin da Amurka ya samo asalinsa ne daga irin akidun da kasar ta Amurka ke da shi. A ganin kasar Amurka, moriyarta, da tsaronta, sun fi muhimmanci fiye da na sauran kasashe. Tana kuma yayata irin salon ’yanci da dimokuradiyya, da hakkin dan Adam nata a duniya, ta yadda duk wata kasar da ba ta yi mata biyayya ba, to za ta dauke ta a matsayin abokiyar gaba, har ma za ta yi kokarin dakile ta, da rushe mulkinta, har ma kaddamar da yaki a kanta, kuma irin wannan misali ba ya lasaftuwa.

Kasar Sin a nata bangaren tana daukar matsayi akasin haka, inda ta gabatar da shawarar “raya daukacin kasashen duniya baki daya”, shawarar da ta jaddada muhimmancin rashin barin wata kasa a baya, baya ga kuma shawarar “kiyaye tsaron bai daya na kasashen duniya” da kasar ta gabatar, wadda ta jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya da tsaro na bai daya na daukacin kasashen duniya. Sai kuma shawarar “raya mabambantan wayewar kai na duniya” da kasar Sin ta gabatar, wadda ta jaddada muhimmancin martaba kasancewar mabambantan wayewar kai a duniya.

Manufofi mabanbanta da Amurka da Sin ke yayatawa, na da nasaba ne da banbancin tunani. Amurka a bangaren ta, na da imanin cewa, idan wani ya samu kudi, hakan na nufin wani zai rasa nasa, yayin da a nata bangare kasar Sin ke ganin mutane da dama, na iya ci daga kwarya guda, sabo da za a iya girka abincin da zai ishi kowa. Bugu da kari, Amurka na ganin ba zai yiwu teku daya ya ishi manyan kasashe biyu wanka ba; A daya bangaren kuma, Sin na ganin wannan duniya ta ishi kowa watayawa, da samun ci gaban bai daya, da wadatar daukacin kasashen duniya, ciki har da Sin da ita kan ta Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

Kafin Madam Yellen ta tashi zuwa kasar Sin, wani dan jarida da ya bi ta a wannan ziyara, ya wallafa wata makala mai taken “Yellen za ta kai ziyara kasar Sin don daidaita dangantakar tattalin arziki tsakanin kasashen biyu” a jaridar “New York Times”, kuma a bangaren ra’ayoyin masu karatu, akwai Amurkawa da suka karanta makalar da suka bayyana cewa, da fatan Yellen za ta bude sabon babi da kasar Sin, sabo da Sin da Amurka ba su bukatar zama abokan gaba ga juna.

Abin haka yake. A hakika, Sin da Amurka sun kasance suna cin moriyar juna a huldarsu ta tattalin arziki, kuma kowanensu ba zai amfana da yakin ciniki ko rarrabuwar kawuna a tsakaninsu ba, kuma abu ne mai kyau kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya su zauna su yi musayar ra’ayi da juna.

Madam Yellen na ci gaba da wannan ziyara a kasar Sin, mu kuma muna zuba ido don gani abin da za ta fada, musamman abin da za ta aikata daga baya.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bangare Japan Da Ya Dage Sai Ya Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya Cikin Teku Zai Sha Kunya Ta Tsawon Tarihi

Next Post

‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

Related

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

45 minutes ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

2 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

3 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

4 hours ago
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
Daga Birnin Sin

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

24 hours ago
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

1 day ago
Next Post
‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

August 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

August 8, 2025
Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.