ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Yanzu haka sakatariyar baitulmalin kasar Amurka Janet Yellen na yin ziyarar aiki ta kwanaki hudu a kasar Sin, wadda kuma ta kasance ta biyu daga cikin manyan jami’an gwamnatin Biden da suka kawo ziyara a kasar Sin, biyo bayan ziyarar da sakataren harkokin wajen kasar Antony Blinken ya yi a watan da ya gabata. A labarin da aka bayar, an ce, da mista Antony Blinken da Madam Yellen dukkansu sun bayyana cewa, Amurka na son tabbatar da daidaiton da shugabannin kasashen biyu suka cimma a yayin ganawarsu a gefen taron kolin G20, wanda aka gudanar a bara a tsibirin Bali na kasar Indonesia, wato su martaba juna, da zama lafiya da juna, da kuma yi hadin gwiwa ta cin moriyar juna, kuma Amurka ba ta son ganin rarrabuwar kawuna a tsakaninta da kasar Sin. 

Amurka ta tura manyan jami’anta zuwa kasar Sin tare da yin kalaman da suka kasance tamkar neman kyautata hulda da kasar Sin, sai dai ba lallai al’amarin haka yake ba, kasancewar bayan da mista Blinken ya koma gida, ya bayyana wa ’yan jarida cewa, “sabanin dake tsakanin Sin da Amurka ba wani boyayyen abu ba ne. Kuma Amurka za ta ci gaba da kare moriyarta da akidunta, haka kuma za ta ci gaba da yin abin da kasar Sin ba ta son gani, tare da furta abubuwan da Sin din ba ta son ji.”

  • Ziyarar Xi Jinping A Jiangsu Na Da Nufin Inganta Aikin Gina Tsarin Masana’antu Na Zamani Na Kasar Sin

A hakika, sabanin da ke tsakanin Sin da Amurka ya samo asalinsa ne daga irin akidun da kasar ta Amurka ke da shi. A ganin kasar Amurka, moriyarta, da tsaronta, sun fi muhimmanci fiye da na sauran kasashe. Tana kuma yayata irin salon ’yanci da dimokuradiyya, da hakkin dan Adam nata a duniya, ta yadda duk wata kasar da ba ta yi mata biyayya ba, to za ta dauke ta a matsayin abokiyar gaba, har ma za ta yi kokarin dakile ta, da rushe mulkinta, har ma kaddamar da yaki a kanta, kuma irin wannan misali ba ya lasaftuwa.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin a nata bangaren tana daukar matsayi akasin haka, inda ta gabatar da shawarar “raya daukacin kasashen duniya baki daya”, shawarar da ta jaddada muhimmancin rashin barin wata kasa a baya, baya ga kuma shawarar “kiyaye tsaron bai daya na kasashen duniya” da kasar ta gabatar, wadda ta jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya da tsaro na bai daya na daukacin kasashen duniya. Sai kuma shawarar “raya mabambantan wayewar kai na duniya” da kasar Sin ta gabatar, wadda ta jaddada muhimmancin martaba kasancewar mabambantan wayewar kai a duniya.

Manufofi mabanbanta da Amurka da Sin ke yayatawa, na da nasaba ne da banbancin tunani. Amurka a bangaren ta, na da imanin cewa, idan wani ya samu kudi, hakan na nufin wani zai rasa nasa, yayin da a nata bangare kasar Sin ke ganin mutane da dama, na iya ci daga kwarya guda, sabo da za a iya girka abincin da zai ishi kowa. Bugu da kari, Amurka na ganin ba zai yiwu teku daya ya ishi manyan kasashe biyu wanka ba; A daya bangaren kuma, Sin na ganin wannan duniya ta ishi kowa watayawa, da samun ci gaban bai daya, da wadatar daukacin kasashen duniya, ciki har da Sin da ita kan ta Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Kafin Madam Yellen ta tashi zuwa kasar Sin, wani dan jarida da ya bi ta a wannan ziyara, ya wallafa wata makala mai taken “Yellen za ta kai ziyara kasar Sin don daidaita dangantakar tattalin arziki tsakanin kasashen biyu” a jaridar “New York Times”, kuma a bangaren ra’ayoyin masu karatu, akwai Amurkawa da suka karanta makalar da suka bayyana cewa, da fatan Yellen za ta bude sabon babi da kasar Sin, sabo da Sin da Amurka ba su bukatar zama abokan gaba ga juna.

Abin haka yake. A hakika, Sin da Amurka sun kasance suna cin moriyar juna a huldarsu ta tattalin arziki, kuma kowanensu ba zai amfana da yakin ciniki ko rarrabuwar kawuna a tsakaninsu ba, kuma abu ne mai kyau kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya su zauna su yi musayar ra’ayi da juna.

Madam Yellen na ci gaba da wannan ziyara a kasar Sin, mu kuma muna zuba ido don gani abin da za ta fada, musamman abin da za ta aikata daga baya.

 

 

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Next Post
‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.