• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

More Ci Gaba Tare Wata Babbar Manufa Ce Ta Kasar Sin 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
More Ci Gaba Tare Wata Babbar Manufa Ce Ta Kasar Sin 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya, wasu dalibai ’yan Najeriya 65 sun kammala karatu a kasar Sin, sun kuma koma gida. Bisa tallafin da wani kamfanin kasar Sin ya ba su, wadannan dalibai sun gama karatun ilimin injiniyan gini, da fannin jigilar kayayyaki a jami’o’in kasar Sin, inda suka samu digiri na farko ko na biyu. Galibinsu za su fara aiki a kamfanonin kasar Sin dake Najeriya, inda za su samar da gudunmowa ga aikin raya masana’antu masu alaka da zirga-zirgar jiragen kasa a kasarsu ta Najeriya.

Batun nan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin taimakawa Najeriya wajen samun ci gaba. Ban da daukar nauyin gina layin dogo na Abuja-Kano, da na Lagos-Ibadan, da layin jirgin kasa a birnin Abuja, da dai sauran ingantattun kayayyakin more rayuwa a Najeriya, kasar Sin ta kuma ba da taimako a fannin horar da kwararrun da suka san yadda ake sarrafawa da kulawa da kayayyakin. Ban da haka kuma, kasar ta mika wa matasan Najeriya damammaki na samun ilimi, da guraben aikin yi, da na cimma manyan burikan da suka sanya a gaba.

  • Sin Da Amurka Na Da Bukatar Karfafa Hadin Gwiwa, In Ji Firaministan Kasar Sin

Hakika, idan mun yi tsokaci kan manufofin kasar Sin na hulda da sauran kasashe, za mu ga yadda “more ci gaba tare” ya kasance wani muhimmin bangare a cikinsu. Cikin “shawarar neman samun ci gaba a duk duniya” wadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, ya ambaci fannonin da suka hada da taimakawa sauran kasashe masu tasowa samun ci gaban tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama’arsu, da hadin kai da sauran kasashe a kokarin rage talauci, da tabbatar da samar da isashen abinci, da samar da jarin da ake bukata don neman ci gaba, da raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da raya masana’antu, da dai makamantansu.

Ban da haka kuma, kasar Sin ta daukaka tunanin “Kyan alkawari cikawa”. Tun da ta ba da shawarar “more ci gaba tare”, to, dole ne ta yi kokarin aiwatar da manufar. Game da haka, za a iya duba abubuwan dake faruwa a dab da mu, wadanda suka kasance misalai ga yadda hadin gwiwa tare da kasar Sin ke haifar da ci gaba ga kasashen Afirka:

A kasar Mauritius dake gabashin Afirka, wani kamfanin kasar Sin ya gina wata madatsar ruwa a dab da birnin Port Louis na kasar, wadda ta kawo karshen matsalar karancin ruwa da birnin ke fuskanta, ta yadda mazauna wurin suke iya samun ruwan famfo. Wannan shi ne misalin yadda ake samun ingantuwar zaman rayuwar jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

A kasar Kenya kuma, layin dogon da aka gina a tsakanin Mombasa da Nairobi, ya rage lokacin zirga-zirga a tsakanin biranen daga sa’o’i 10 zuwa sa’o’i 4. Ya kuma sanya ‘yan kasuwan kasar murna sosai, domin kudin da suke kashewa wajen jigilar kaya ya ragu da kashi 79%. Hakan misali ne na kyautatuwar muhallin ciniki, da aka samu ta hanyar hadin gwiwa da kasar Sin.

Haka zalika, cikin shekaru fiye da goma da suka gabata, ta hanyar gudanar da kwas na gajeren lokaci, kasar Sin ta taimaki kasashen Afirka wajen horar da mutane fiye da dubu 300, wadanda suka zama kwararru a fannonin aikin gona, da kula da itatuwa, da kare muhalli, da dai sauransu. Wannan ya nuna yadda kasar Sin take taimakawa kasashen Afirka wajen samun karfin raya tattalin arziki ta hanyar dogaro da kai.

Ko a nahiyar Afirka, ko a sauran wurare da kusurwoyin duniya, za a iya ganin dimbin misalai iri daya da wadanda muka ambata. Sai dai me ya sa kasar Sin ke son yayata ra’ayin “more ci gaba tare” a duniya?

Dalilin da ya sa haka shi ne al’adun gargajiyar kasar. Kaka da kakanin Sinawa, musamman ma wasu shahararrun malamai masu ilimi sun taba bayyana cewa, “ Duk wani abun da ba ka so, kar ka yi shi kan sauran mutane”, kana “ Mutum mai kirki ya fi dora muhimmanci kan kare adalci maimakon moriyar kai”. Ban da haka kuma, sun ce, “A yayin da kake kula da tsoffi da yara dake gidanka, kar ka manta da taimakon tsoffi da yara na gidajen sauran mutane.” Wannan tunani da al’adu mai alaka da shi sun sa Sinawa darajanta yanayin daidato, da adalci, da more alheri tare, gami da samun jituwa.

Sa’an nan wannan nau’in al’adu na gargajiya ya tabbatar da cewa, kasar Sin ba za ta mai da moriyar kanta a gaban ta sauran kasashe ba, kuma ba za ta taba neman yin babakere a duniya ba. Bayan da kasar ta samu nasarar raya kanta daga wata kasa mai talauci zuwa kasa mai karfin tattalin arziki tattalin arziki ta biyu a duniya, tare da samun dimbin fasahohi a fannin neman ci gaba, kasar na kuma son raba fasahohinta da sauran kasashe, da hadin gwiwa da su don neman damar samun ci gaban tattalin arziki na bai daya. Saboda bisa tunanin Sinawa, duniya ba za ta zama mai kyau ba, har sai an tabbatar da dadaito, da zaman lafiya, da more ci gaba, da wayewar kai a cikinta. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Ghana: Ci Gaban Sin A Fannin Noma Da Yaki Da Fatara Na Karfafa Gwiwar Sauran Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

17 hours ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

18 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

20 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

22 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

23 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

2 days ago
Next Post
Kasar Sin

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

May 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.