• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Messi

Za a iya cewa a baya an ga Messin Iran da Messin Jamus da Messin Scottland da wasu masu yawa amma yanzu lokaci ne da za a ce barka ga Messin Turkiyya, wato Arda Guler.

Yaron da ake kwatantawa da gwarzon Argentina Lionel Messi yanzu ya sha kan mafi yawan matasan ‘yan wasa, musamman wadanda suka kware wajen yanka da wasa da kwallo, wani abu da dan wasan mai shekara 18 ya kware a kai.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Cire Tallafin Fetur: Tinubu Na Neman Sahalewar Majalisar Wakilai Don Samar Da Kudaden Rage Radadi

Kawo yanzu babu wani dan wasa da ya kai inda matashin ya kai, cikin wadanda suka gabace shi kamar su Sardar Azmoun da Marko Marin da kuma Ryan Gauld. Duka babu wanda ya yi kusa.

Akwai kwarin gwiwar matashin dan wasan mai basira Guler zai iya zama daya daga cikin fitattun ‘yan wasan da za su yi suna a duniya, a yanzu kuma kaddara na neman kai shi gasar da mutumin da ake kwatanta shi da shi ya buga a kungiyar da ya yi adawa da ita.

Tun daga lokacin da ya fara buga wa tawagar Fenerbache wasan farko, manyan kungiyoyin kwallon kafa na Turai suka fara bayyana maitarsu a fili kan matashin dan wasan.

LABARAI MASU NASABA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Kungiyar da Messi ya buga wa kwallo Barcelona ta nuna muradinta a fili na daukar dan wasan, kuma shugaban kungiyar Joan Laporta ya aika daraktan wasannin kungiyar Deco domin ya tattauna kan batun.

Sai dai abu ne mara dadi ga kungiyar ta Barcelona ganin yadda dan wasan ya zabi babbar abokiyar hamayyarta a matsayin wadda yake so maimakon ita, ya koma Real Madrid a matsayin mafi basira daga yankinsu da ya buga kwallo a Bernabeu.

Wani abu da ya burge masu dillancin dan wasan shi ne yadda kungiyoyi suka yi ca a kan dan wasan – irin su Bayern Munich da Borussia Dortmund da Paris St-Germain da kuma uku daga Premier Ingila Arsenal da Manchester United da Newcastle.

Rahotanni sun bayyana cewa an ta taya shi yuro milyan 17.5, abin da ya sanya ba shi damar kara buga wasanni masu yawa a kungiyarsa, kuma wannan wani dan wasa ne da aka amince ya fara yi wa babbar kungiyarsa wasa a shekaru 16, inda ya shiga a matsayin canji a minti na 66 a wasan da Fenerbache ta yi nasara a HJK Helsinki 1-0 a wasan farko na neman shiga gasar Europa a ranar 19 ga watan Agustan 2021.

Yaron da ya bayar da kwallo aka ci a wasan Super Lig na farko, ya zama dan wasa mafi karancin shekaru da ya ci kwallo a wasan 5-2 a ranar 13 ga watan Maris 2022, kwana 16 daga shigar sa shekara ta 17.

Duka dai, yana da kwallo bakwai ya kuma ba da bakwai an ci a minti 1,187 na Super Lig da ya buga, ma’ana ya yi wani abu na cin kwallo a kowanne minti 85 na wasan kamar yadda kididdiga ta nuna.

Ba shi lamba 10 da aka yi a Fenerbache na nuni da yadda ya samu shiga cikin kungiyar sosai saboda rigar da a baya manyan ‘yan wasa irin su Tuncay Sanli da Robin ban Persie da kuma Mesut Ozil, mafi mahimmanci shi ne Aled gwarzon kungiyar ta Istanbul wanda ya ci kwallo 171 ya ba da 136 aka ci a wasa 344 tsakanin 2004 zuwa 2012 kuma aka yi mutum-mutuminsa a wani wuri a garin.

Idan har za’a iya kwatanta Guler da wani dan wasa shi ne tsohon dan Brazil din, a karshe, ba ya fargabar gwada wani abu, misali shi ne kwallo da ya ci daga wajen yadi na 20 a wasan da suka ci 5 -1 a watan Janairu da Kasimpasa.

Ya yi wasansa na farko a kasa a wasan sada zumunta da suka yi da Jamhuriyar Czech a ranar 19 da watan Nuwamba 2022, ya ci kwallonsa ta farko a watan Yunin nan da ya gabata, a wasansa na hudu.

Abin tambayar a nan shi ne, wannan lokacin shi ne mafi dacewa ga dan wasan ya tsallaka mataki na gaba a rayuwar kwallonsa? Tsohon dan wasan gaban Fenerbache, Ozil, wanda Guler ya gada, wanda ya tafi Real Madrid, yana da shekara 21, ya shawarci matashin da ya kara shekara guda a Turkiyya domin kara samun gogewa.

Da alama dai wannan cinikin da Real Madrid ke yi tana kara neman hada wasu sabbin zubi na Galacticos saboda akwai ‘yan wasan gaba masu tashe, Binicius Jr da Rodrygo da suke a kungiyar dama.

Idan har shirin Real Madrid ya tafi yadda take so kungiyar za ta cika da matasa kuma hazikan ‘yan kwallo, irin su Aurelien Tchoumameni da Eduardo Camabinga da Jude Bellingham a tsakiyar kungiyar sai kuma watakila Kylian Mbappe, idan har ya koma kungiyar a yanzu ko kuma a karshen kakar nan da za’a fara wato shekara ta 2024.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya
Wasanni

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba
Wasanni

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa
Wasanni

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Next Post
Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.