ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Messi

Za a iya cewa a baya an ga Messin Iran da Messin Jamus da Messin Scottland da wasu masu yawa amma yanzu lokaci ne da za a ce barka ga Messin Turkiyya, wato Arda Guler.

Yaron da ake kwatantawa da gwarzon Argentina Lionel Messi yanzu ya sha kan mafi yawan matasan ‘yan wasa, musamman wadanda suka kware wajen yanka da wasa da kwallo, wani abu da dan wasan mai shekara 18 ya kware a kai.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Cire Tallafin Fetur: Tinubu Na Neman Sahalewar Majalisar Wakilai Don Samar Da Kudaden Rage Radadi

Kawo yanzu babu wani dan wasa da ya kai inda matashin ya kai, cikin wadanda suka gabace shi kamar su Sardar Azmoun da Marko Marin da kuma Ryan Gauld. Duka babu wanda ya yi kusa.

ADVERTISEMENT

Akwai kwarin gwiwar matashin dan wasan mai basira Guler zai iya zama daya daga cikin fitattun ‘yan wasan da za su yi suna a duniya, a yanzu kuma kaddara na neman kai shi gasar da mutumin da ake kwatanta shi da shi ya buga a kungiyar da ya yi adawa da ita.

Tun daga lokacin da ya fara buga wa tawagar Fenerbache wasan farko, manyan kungiyoyin kwallon kafa na Turai suka fara bayyana maitarsu a fili kan matashin dan wasan.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Kungiyar da Messi ya buga wa kwallo Barcelona ta nuna muradinta a fili na daukar dan wasan, kuma shugaban kungiyar Joan Laporta ya aika daraktan wasannin kungiyar Deco domin ya tattauna kan batun.

Sai dai abu ne mara dadi ga kungiyar ta Barcelona ganin yadda dan wasan ya zabi babbar abokiyar hamayyarta a matsayin wadda yake so maimakon ita, ya koma Real Madrid a matsayin mafi basira daga yankinsu da ya buga kwallo a Bernabeu.

Wani abu da ya burge masu dillancin dan wasan shi ne yadda kungiyoyi suka yi ca a kan dan wasan – irin su Bayern Munich da Borussia Dortmund da Paris St-Germain da kuma uku daga Premier Ingila Arsenal da Manchester United da Newcastle.

Rahotanni sun bayyana cewa an ta taya shi yuro milyan 17.5, abin da ya sanya ba shi damar kara buga wasanni masu yawa a kungiyarsa, kuma wannan wani dan wasa ne da aka amince ya fara yi wa babbar kungiyarsa wasa a shekaru 16, inda ya shiga a matsayin canji a minti na 66 a wasan da Fenerbache ta yi nasara a HJK Helsinki 1-0 a wasan farko na neman shiga gasar Europa a ranar 19 ga watan Agustan 2021.

Yaron da ya bayar da kwallo aka ci a wasan Super Lig na farko, ya zama dan wasa mafi karancin shekaru da ya ci kwallo a wasan 5-2 a ranar 13 ga watan Maris 2022, kwana 16 daga shigar sa shekara ta 17.

Duka dai, yana da kwallo bakwai ya kuma ba da bakwai an ci a minti 1,187 na Super Lig da ya buga, ma’ana ya yi wani abu na cin kwallo a kowanne minti 85 na wasan kamar yadda kididdiga ta nuna.

Ba shi lamba 10 da aka yi a Fenerbache na nuni da yadda ya samu shiga cikin kungiyar sosai saboda rigar da a baya manyan ‘yan wasa irin su Tuncay Sanli da Robin ban Persie da kuma Mesut Ozil, mafi mahimmanci shi ne Aled gwarzon kungiyar ta Istanbul wanda ya ci kwallo 171 ya ba da 136 aka ci a wasa 344 tsakanin 2004 zuwa 2012 kuma aka yi mutum-mutuminsa a wani wuri a garin.

Idan har za’a iya kwatanta Guler da wani dan wasa shi ne tsohon dan Brazil din, a karshe, ba ya fargabar gwada wani abu, misali shi ne kwallo da ya ci daga wajen yadi na 20 a wasan da suka ci 5 -1 a watan Janairu da Kasimpasa.

Ya yi wasansa na farko a kasa a wasan sada zumunta da suka yi da Jamhuriyar Czech a ranar 19 da watan Nuwamba 2022, ya ci kwallonsa ta farko a watan Yunin nan da ya gabata, a wasansa na hudu.

Abin tambayar a nan shi ne, wannan lokacin shi ne mafi dacewa ga dan wasan ya tsallaka mataki na gaba a rayuwar kwallonsa? Tsohon dan wasan gaban Fenerbache, Ozil, wanda Guler ya gada, wanda ya tafi Real Madrid, yana da shekara 21, ya shawarci matashin da ya kara shekara guda a Turkiyya domin kara samun gogewa.

Da alama dai wannan cinikin da Real Madrid ke yi tana kara neman hada wasu sabbin zubi na Galacticos saboda akwai ‘yan wasan gaba masu tashe, Binicius Jr da Rodrygo da suke a kungiyar dama.

Idan har shirin Real Madrid ya tafi yadda take so kungiyar za ta cika da matasa kuma hazikan ‘yan kwallo, irin su Aurelien Tchoumameni da Eduardo Camabinga da Jude Bellingham a tsakiyar kungiyar sai kuma watakila Kylian Mbappe, idan har ya koma kungiyar a yanzu ko kuma a karshen kakar nan da za’a fara wato shekara ta 2024.

Messi
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Yadda FIFA Ta Yi Yunƙurin Sasanta Rikicin Israila Da Amurka A Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.