• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a iya cewa a baya an ga Messin Iran da Messin Jamus da Messin Scottland da wasu masu yawa amma yanzu lokaci ne da za a ce barka ga Messin Turkiyya, wato Arda Guler.

Yaron da ake kwatantawa da gwarzon Argentina Lionel Messi yanzu ya sha kan mafi yawan matasan ‘yan wasa, musamman wadanda suka kware wajen yanka da wasa da kwallo, wani abu da dan wasan mai shekara 18 ya kware a kai.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Cire Tallafin Fetur: Tinubu Na Neman Sahalewar Majalisar Wakilai Don Samar Da Kudaden Rage Radadi

Kawo yanzu babu wani dan wasa da ya kai inda matashin ya kai, cikin wadanda suka gabace shi kamar su Sardar Azmoun da Marko Marin da kuma Ryan Gauld. Duka babu wanda ya yi kusa.

Akwai kwarin gwiwar matashin dan wasan mai basira Guler zai iya zama daya daga cikin fitattun ‘yan wasan da za su yi suna a duniya, a yanzu kuma kaddara na neman kai shi gasar da mutumin da ake kwatanta shi da shi ya buga a kungiyar da ya yi adawa da ita.

Tun daga lokacin da ya fara buga wa tawagar Fenerbache wasan farko, manyan kungiyoyin kwallon kafa na Turai suka fara bayyana maitarsu a fili kan matashin dan wasan.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Kungiyar da Messi ya buga wa kwallo Barcelona ta nuna muradinta a fili na daukar dan wasan, kuma shugaban kungiyar Joan Laporta ya aika daraktan wasannin kungiyar Deco domin ya tattauna kan batun.

Sai dai abu ne mara dadi ga kungiyar ta Barcelona ganin yadda dan wasan ya zabi babbar abokiyar hamayyarta a matsayin wadda yake so maimakon ita, ya koma Real Madrid a matsayin mafi basira daga yankinsu da ya buga kwallo a Bernabeu.

Wani abu da ya burge masu dillancin dan wasan shi ne yadda kungiyoyi suka yi ca a kan dan wasan – irin su Bayern Munich da Borussia Dortmund da Paris St-Germain da kuma uku daga Premier Ingila Arsenal da Manchester United da Newcastle.

Rahotanni sun bayyana cewa an ta taya shi yuro milyan 17.5, abin da ya sanya ba shi damar kara buga wasanni masu yawa a kungiyarsa, kuma wannan wani dan wasa ne da aka amince ya fara yi wa babbar kungiyarsa wasa a shekaru 16, inda ya shiga a matsayin canji a minti na 66 a wasan da Fenerbache ta yi nasara a HJK Helsinki 1-0 a wasan farko na neman shiga gasar Europa a ranar 19 ga watan Agustan 2021.

Yaron da ya bayar da kwallo aka ci a wasan Super Lig na farko, ya zama dan wasa mafi karancin shekaru da ya ci kwallo a wasan 5-2 a ranar 13 ga watan Maris 2022, kwana 16 daga shigar sa shekara ta 17.

Duka dai, yana da kwallo bakwai ya kuma ba da bakwai an ci a minti 1,187 na Super Lig da ya buga, ma’ana ya yi wani abu na cin kwallo a kowanne minti 85 na wasan kamar yadda kididdiga ta nuna.

Ba shi lamba 10 da aka yi a Fenerbache na nuni da yadda ya samu shiga cikin kungiyar sosai saboda rigar da a baya manyan ‘yan wasa irin su Tuncay Sanli da Robin ban Persie da kuma Mesut Ozil, mafi mahimmanci shi ne Aled gwarzon kungiyar ta Istanbul wanda ya ci kwallo 171 ya ba da 136 aka ci a wasa 344 tsakanin 2004 zuwa 2012 kuma aka yi mutum-mutuminsa a wani wuri a garin.

Idan har za’a iya kwatanta Guler da wani dan wasa shi ne tsohon dan Brazil din, a karshe, ba ya fargabar gwada wani abu, misali shi ne kwallo da ya ci daga wajen yadi na 20 a wasan da suka ci 5 -1 a watan Janairu da Kasimpasa.

Ya yi wasansa na farko a kasa a wasan sada zumunta da suka yi da Jamhuriyar Czech a ranar 19 da watan Nuwamba 2022, ya ci kwallonsa ta farko a watan Yunin nan da ya gabata, a wasansa na hudu.

Abin tambayar a nan shi ne, wannan lokacin shi ne mafi dacewa ga dan wasan ya tsallaka mataki na gaba a rayuwar kwallonsa? Tsohon dan wasan gaban Fenerbache, Ozil, wanda Guler ya gada, wanda ya tafi Real Madrid, yana da shekara 21, ya shawarci matashin da ya kara shekara guda a Turkiyya domin kara samun gogewa.

Da alama dai wannan cinikin da Real Madrid ke yi tana kara neman hada wasu sabbin zubi na Galacticos saboda akwai ‘yan wasan gaba masu tashe, Binicius Jr da Rodrygo da suke a kungiyar dama.

Idan har shirin Real Madrid ya tafi yadda take so kungiyar za ta cika da matasa kuma hazikan ‘yan kwallo, irin su Aurelien Tchoumameni da Eduardo Camabinga da Jude Bellingham a tsakiyar kungiyar sai kuma watakila Kylian Mbappe, idan har ya koma kungiyar a yanzu ko kuma a karshen kakar nan da za’a fara wato shekara ta 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arda GulerDan WasaKwallon KafaMessiReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Arsenal Ta Kammala Daukar Timber

Next Post

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

8 hours ago
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Wasanni

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

1 day ago
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
Wasanni

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

2 days ago
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
Wasanni

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

3 days ago
Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

3 days ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin
Wasanni

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

3 days ago
Next Post
Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

Wang Yi Ya Bukaci Amurka Da Ta Dauki Kwararan Matakai Don Dawo Da Alakar Sin Da Amurka Kan Turbar Da Ta Dace       

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.