• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

by Aisha Seyoji
2 years ago
in Ra'ayoyi
0
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

A halin yanzu ‘Yan Nijeriya na ta dakon ganin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada ministocitoci. Shin a ganinka/ki, wane ne mafi cancanta a nada shi Minista daga Jiharku. Fadi suna da kuma takaitaccen bayani kan zabin naka ko naki.

LUKMAN B. ADAM: Pantami Ya Fi Cancanta Daga Gombe

A jiharmu ta Gombe kam gaskiya babu wanda ya cancanta daya wuce Prof Isa Ali Ibrahim Pantami. Domin kuwa shi ne kadai ya san damuwan talakawa kuma yake taimaka musu sannan kuma Mutum ne wanda ba ya kyamar mutane ga kuma ilimi ta kowane bangaren rayuwa da Allah ya ba shi kuma sannan ga shi ya yi mun gani duk Nijeriya tunda ake ba a taba yin Minista da ya yi aikin da ya yi ba.

Kai a takaice dai Nijeriyar ma kanta irin Prof Isa Ali muke bukata ba ‘yan bulkara da karya da rainin hankali ba.

CMRD MOHD GADDAFI AWWAL: El-Rufai Ya Kamata A Nada Daga Kaduna

Gaskiya ni dai a nawa ra’ayin, Malam Nasiru El-Rufai ya fi cancanta a nada daga Kaduna, jajirtacce ne kowa ya san shi, ba ya wasa a kan aikinsa.

SADEEK RUFAI DANGUGUWA: Ina So A Dauki Kwankwaso Daga Kano

Ina son Engr Dr Rabiu Musa Kwankwaso na Jahar Kano ya kasance daya daga cikin Ministocin da za a nada. Ba don komai ba, sai don kyakkyawan yakinin da nake dashi a kansa, saboda Kwankwaso mutum ne mai sanin makamar aiki ta kowacce siga, ba zan riya cewa Kwankwaso ya kai makura ba, domin kaiwa makura siffa ce da Ubangiji Ya kabance kanshi da ita, amma tabbas Kwankwaso na da dukkan ‘Capacity’ din zama daya daga cikin Ministocin kasar nan.

JAFAR S. HASSAN KARABA: Gwamma A Nada Sani Sha’aban A Kaduna

Mu a Kaduna wanda nake ganin ya fi kowa cancanta a nada shi shi ne Sani Sha’aban, shi muke so, saboda ya fi Nasiru sanin hakkin al’umma wallahi.

IT’Z JAMEEL MOHD: Ba Ruwanmu Da Wani Minista, Fatanmu Farashin Kayan Masarufi Ya Sauka

Kullum fata muke farashin kayan masa rufi ya yi kasa talaka ya ji dadi a Nijeriya. Babu ruwanmu da wani minister. Buhun masara 48k, Shinkafa 35k, Litar Mai 600, Ina talakan Nijeriya zai sa kansa?

APC Change Change: Ganduje Da Gawuna Muke So A Nada Daga Kano

A gaskiya mu dai a ganinmu babu wanda ya cancanta a nada a matsayin minister daga Jihar Kano illa Ganduje da Gawuna.

ABDUL’AZIZ MOHAMMED: Allah Ya Zaba Mana Mafi Alheri Daga Gombe

Da farko dai ina miki barka da wannan lokaci, Allah ya datar da mu amin. Ni dai a nawa bangaren a gaskiya addu’a nake, duk wanda zai zama alkhairi ga al’ummar Jihar Gombe da ma kasa gaba daya Allah ya tabbatar mana da shi amin.

ALIYU SULAIMAN: A Nada Mana Isah Yuguda Daga Jihar Bauchi

Ni dai nawa zabin a Jihar Bauchi shi ne: Isah Yuguda. Sabida a Bauchi babu wanda bai san Jarumtarsa ba. A lokachin Isah Yuguda a Bauchi, ‘Principal’ din ‘Secondary school’ ma na hawa mota. Amma ban da zamanin Bala. Ya yi minista a baya na ‘abiation’, an ga rawar da ya taka. Yanzu ma idan ya samu dama, zai sake yin abin da ya saba. Sabida shi dan mai kishin mutanensa ne a zuciya.

UMAR ABDULLAHI: Allah Ya Sa A Nada Mana Hazikai

Ina miki fatan alkhairi, Allah ya sa mu dai a sa mana hazikai masu aikin da aka nada su wanda za mu ga canji na alkhairi a kasarmu Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistociTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024

Next Post

Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano – Yadakwari

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

5 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

9 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

10 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

10 months ago
BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

10 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

11 months ago
Next Post
Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano – Yadakwari

Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano - Yadakwari

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.