• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Akwa Ibom ta gurfanar da wani mutum mai suna Aniekan James bisa zarginsa da kashe dansa guda daya tilo da Allah ya ba shi, Odudu James, mai shekara 35 a duniya.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ya gurfanar wanda ake zargin da wasu 268 da aka kama bisa zargin aikata laifuka daban-daban, ana kuma zargin Aniekan da kashe wasu da dama a Legas da Jihar Abia.

  • Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu
  • Ziyarar Firaministan Kasar Tsibiran Solomon A Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana Ga Kasar

Kwamishinan ya ce, jami’an hukumar na caji ofis din Ukanafun ne suka cafke wanda ake zargin a ranar 16 ga watan Yunin 2023.

 Ya ce, “A ranar 16 ga watan Yunin 2023 ne jami’an caji ofis din Ukanafun suka cafke wani mutum Aniekan James na kauyen Ikot Ndot da ke karamar hukumar Ukanafun bisa laifin harbe dansa mai shekara 35, Odudu James, sakamakon cacar baki da ta shiga tsakaninsu. Ana zargin wanda aka kama din da aikata laifukan kisan mutane da dama a jihohin Legas da Abia.”

Kazalika, kwamishinan ya kuma gurfanar da wani bisa zargin yin garkuwa da mukaddashin shugaban wata jami’a mai zaman kanta da aka sace a lokacin da yake hanyarsa ta komawa gida.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Ya ce, sauran miliyan biyu na kudin fansa da mota kirar Toyota Corolla da aka yi amfani da su wajen aikata laifin an kwato su yayin da shugaban makarantar ya koma cikin iyalansa.

Ya ce an yi garkuwa da mataimakin shugaban jami’ar ne a ranar 14 ga watan Afrilun 2023 a lokacin da ke hanyarsa ta komawa gida. Amma bayan kwana biyu da sace shi, rundunar ra kama wani mai suna Prince Thursday Okon wani tsohon ma’aikacin babban malamin din ne da zargin shi ne ya sace shugaban makarantar.

“An kori Okon daga aiki bisa zargin aikata manyan laifuka. An kama shi ne tare da abokan aikata laifukansu biyu, Sabiour Sunday Luke da Richard Friday, dukkaninsu ‘yan kauyen Ikot Ebam da ke karamar hukumar Mkpan Enin.”

Har-ila-yau, an gurfanar da wani Edu Ime bisa zarginsa da zama mamba na kungiyar asiri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cacar-bakiDaKisaMahaifi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu

Next Post

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

4 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

3 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

3 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

4 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.