ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
Amince

A watan Satumba ne Faransa za ta amince da kafa ƙasar Falasɗinawa a hukumance, kamar yadda Shugaba Emmanuel Macron ya sanar, hakan kuma ya sa Faransa ta zama ƙasar G7 ta farko da ta yi hakan.

A wani saƙo a shafin ɗ, Macron ya bayyana cewa a wani zama da za a yi a zauren Majalisar da ke New York ne za a ayyana hakan a hukumance.

“Buƙatar gaggawa a yau ita ce a kawo ƙarshen yaƙin Gaza a kuma samu kuɓutar da farar hular da ke zirin. Zaman lafiya abu ne mai yiwuwa. Muna buƙatar a gaggauta tsagaita wuta, a saki mutanen da ke tsare a kuma kai wa mutanen Gaza gagarumin agajin jin ƙai,” kamar yadda ya rubuta.

ADVERTISEMENT
  • Masallacin Ƙudus Na Musulmin Duniya Ne – Mabiya Shi’a
  • Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 

Jami’an Falasɗinawa sun yi maraba da matakin Macron yayin da Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce matakin kamar nuna goyon baya ne ga masu ta’addanci sakamakon hare-haren ranar 7 ga watan Oktoban 2023 da Hamas ta kai kan Isra’ila.

Amurka, da kakkausar murya ita ma ta yi fatali da sanarwar Macron, in ji Sakatare harkokin wajenta Marco Rubio, yana bayyana matakin a matsayin “ganganci”.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

G7 ƙungiyar ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki wadda ta ƙunshi Faransa da Amurka da Birtaniya da Italiya da Jamus da Canada da kuma Japan.

Isra’ila ba ta amince da samar da kasar Falasdinawa ba a Gabar yamma da Kogin Jordan da Gaza, saboda a tunaninta, kasar za ta zama barazana ga kasantuwar Isra’ila.

Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya rubuta wani sakon ɗ cewa: “Samar da ƙasar Falasɗinawa a irin wannan yanayi zai samar da wata kafar ruguza Isra’ila – ta kasance cikin tashin hankali. Mu gane wani abu: Falasɗinawa ba ƙasa suke so ba kusa da Isra’ila, suna neman ƙasa ne a maimakon Isra’ila.”

Su wane ne suka amince a samar da ƙasar Falasɗinu?

A yanzu, fiye da ƙasashe 140 cikin mambobin Majalisar ɗinkin ɗuniya 193 ne suka amince a samar da ƙasar Falasɗinawa. ciki har da mambobin ƙungiyar ƙasashe Larabawa da ke Majalisar ɗinkin ɗuniya da ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Musulmi da kuma ƙungiyar yan ba-ruwanmu wadanda ba su nuna matsayarsu ba.

Wasu ƙasashen Turai na daga cikinsu har da Sifaniya da Ireland da Norway wadda ta amince da Falasɗinu a matsayin kasa a Mayun 2024. Gabanin haka, ƙasashen Turai ƙalilan ne suka yi haka galibinsu a 1988.

Sai dai babbar mai mara wa Isra’ila baya, Amurka da ƙawayenta har da Birtaniya da Australiya ba su amince da yankin Falasɗinawa a matsayin ƙasa ba. Australiya ta nuna cewa watakila za ta yi haka ne domin ita ma ta shiga sahun masu goyon bayan maslahar ƙasa biyu.

Me ya sa wasu ƙasashen suka ƙi aminta da kafa ƙasar Falasɗinawa?

ƙasashen da suka ki amincewa da ƙasar Falasɗinawa galibi ba sun yi haka ba ne saboda rashin samun yarjejejiya game da matsugunni wanda Isra’ila ta amince da shi ba.

“ɗuk da cewa a baki tana nuna buƙatar a kafa ƙasar Falasdinawa, Amurka ta dage kan batun tattaunawar gaba da gaba tsakanin Isra’ila da Falasɗinawa, abin da ke nufin bai wa isra’ila damar hawa kujerar na ƙi kan bukatun Falasdinawa,” in ji Fawaz Gerges, farfesa a ɓangaren diflomasiyya tsakanin ƙasashe da siyasar Gabas ta Tsakiya a jami’ar London School of Economics.

An soma tattaunawar zaman lafiya a shekarun 1990 daga bisani burin samar da ƙasa biyu, inda Falasɗinawa da Isra’ila za su iya zama gefe da gefe da juna a ƙasashe daban-daban.

Amince
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.