ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
Amince

A watan Satumba ne Faransa za ta amince da kafa ƙasar Falasɗinawa a hukumance, kamar yadda Shugaba Emmanuel Macron ya sanar, hakan kuma ya sa Faransa ta zama ƙasar G7 ta farko da ta yi hakan.

A wani saƙo a shafin ɗ, Macron ya bayyana cewa a wani zama da za a yi a zauren Majalisar da ke New York ne za a ayyana hakan a hukumance.

“Buƙatar gaggawa a yau ita ce a kawo ƙarshen yaƙin Gaza a kuma samu kuɓutar da farar hular da ke zirin. Zaman lafiya abu ne mai yiwuwa. Muna buƙatar a gaggauta tsagaita wuta, a saki mutanen da ke tsare a kuma kai wa mutanen Gaza gagarumin agajin jin ƙai,” kamar yadda ya rubuta.

ADVERTISEMENT
  • Masallacin Ƙudus Na Musulmin Duniya Ne – Mabiya Shi’a
  • Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 

Jami’an Falasɗinawa sun yi maraba da matakin Macron yayin da Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce matakin kamar nuna goyon baya ne ga masu ta’addanci sakamakon hare-haren ranar 7 ga watan Oktoban 2023 da Hamas ta kai kan Isra’ila.

Amurka, da kakkausar murya ita ma ta yi fatali da sanarwar Macron, in ji Sakatare harkokin wajenta Marco Rubio, yana bayyana matakin a matsayin “ganganci”.

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

G7 ƙungiyar ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki wadda ta ƙunshi Faransa da Amurka da Birtaniya da Italiya da Jamus da Canada da kuma Japan.

Isra’ila ba ta amince da samar da kasar Falasdinawa ba a Gabar yamma da Kogin Jordan da Gaza, saboda a tunaninta, kasar za ta zama barazana ga kasantuwar Isra’ila.

Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya rubuta wani sakon ɗ cewa: “Samar da ƙasar Falasɗinawa a irin wannan yanayi zai samar da wata kafar ruguza Isra’ila – ta kasance cikin tashin hankali. Mu gane wani abu: Falasɗinawa ba ƙasa suke so ba kusa da Isra’ila, suna neman ƙasa ne a maimakon Isra’ila.”

Su wane ne suka amince a samar da ƙasar Falasɗinu?

A yanzu, fiye da ƙasashe 140 cikin mambobin Majalisar ɗinkin ɗuniya 193 ne suka amince a samar da ƙasar Falasɗinawa. ciki har da mambobin ƙungiyar ƙasashe Larabawa da ke Majalisar ɗinkin ɗuniya da ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Musulmi da kuma ƙungiyar yan ba-ruwanmu wadanda ba su nuna matsayarsu ba.

Wasu ƙasashen Turai na daga cikinsu har da Sifaniya da Ireland da Norway wadda ta amince da Falasɗinu a matsayin kasa a Mayun 2024. Gabanin haka, ƙasashen Turai ƙalilan ne suka yi haka galibinsu a 1988.

Sai dai babbar mai mara wa Isra’ila baya, Amurka da ƙawayenta har da Birtaniya da Australiya ba su amince da yankin Falasɗinawa a matsayin ƙasa ba. Australiya ta nuna cewa watakila za ta yi haka ne domin ita ma ta shiga sahun masu goyon bayan maslahar ƙasa biyu.

Me ya sa wasu ƙasashen suka ƙi aminta da kafa ƙasar Falasɗinawa?

ƙasashen da suka ki amincewa da ƙasar Falasɗinawa galibi ba sun yi haka ba ne saboda rashin samun yarjejejiya game da matsugunni wanda Isra’ila ta amince da shi ba.

“ɗuk da cewa a baki tana nuna buƙatar a kafa ƙasar Falasdinawa, Amurka ta dage kan batun tattaunawar gaba da gaba tsakanin Isra’ila da Falasɗinawa, abin da ke nufin bai wa isra’ila damar hawa kujerar na ƙi kan bukatun Falasdinawa,” in ji Fawaz Gerges, farfesa a ɓangaren diflomasiyya tsakanin ƙasashe da siyasar Gabas ta Tsakiya a jami’ar London School of Economics.

An soma tattaunawar zaman lafiya a shekarun 1990 daga bisani burin samar da ƙasa biyu, inda Falasɗinawa da Isra’ila za su iya zama gefe da gefe da juna a ƙasashe daban-daban.

Amince
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz
Kasashen Ketare

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe
Kasashen Ketare

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
Next Post
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.