• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matasa Sun Kone Ofishin Jakadancin Sweden A Iraki Kan Kona Alkur’ani Mai Tsarki

by Sadiq
2 years ago
Sweden

Daruruwan masu zanga-zanga ne suka mamaye ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza, babban birnin kasar Iraki saboda kone wani Alkur’ani mai tsarki da aka yi a Stockholm, babban birnin kasar Sweden.

Masu zanga-zangar sun zagaye katangar ginin da sanyin safiyar ranar Alhamis tare da cinna mata wuta.

  • An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa
  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

Zanga-zangar ta zo ne makonni bayan Salwan Momika, dan kasar Iraki mai shekaru 37 da haihuwa, wanda ya tsere zuwa kasar Sweden shekaru da dama, ya kone wasu shafukan littafin Alkur’ani mai tsarki, a daidai lokacin da musulmi suke gudanar da bukukuwan Idin babbar sallah a watan Yuni.

Matakin na Momika ya jawo kakkausar suka daga kasashe da dama, inda Muqtada Sadr, wani malamin Shi’a mai fada a ji a Iraki, ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar adawa da Sweden tare da korar jakadan Sweden.

An gudanar da zanga-zanga guda biyu a wajen ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza bayan kone Alkur’ani, inda masu zanga-zangar suka keta harabar ofishin jakadancin.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

A ranar Laraba, ‘yansandan Sweden sun ba da takardar neman “taron jama’a” ga mutane biyu a wajen ofishin jakadancin Iraki a Stockholm a ranar Alhamis.

Ko da yake ‘yansanda ba su bayyana abin da masu zanga-zangar ke shirin yi ba, kafafen yada labaran Sweden sun ruwaito cewa mutanen biyu ciki har da Momika sun shirya kone Alkur’ani da tutar Iraki a wurin taron jama’ar.

Da take mayar da martani akan sabuwar zanga-zangar, ma’aikatar harkokin wajen Sweden ta ce dukkan ma’aikatan ofishin jakadancin Bagadaza suna cikin koshin lafiya, tare da yin Allah wadai da harin.

Har ila yau ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta nuna rashin jin dadi kan harin da aka kai ofishin jakadancin kasar Sweden, inda ta yi alkawarin gurfanar da wadanda suka kai harin a gaban kuliya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
‘Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

'Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.