ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Zamfara

Wasu daga cikin ‘yan majalisar jihar Zamfara sun ce babu wani dalili da zai sa gwamnatin jihar ta yi sulhu da ‘yan fashi a jihar.

Honarabul Hamisu A Faru, mai wakiltar mazabar Bukkuyum ta Kudu a majalisar dokokin jihar ne, ya bayyana hakan cikin hirarsa da BBC Hausa.

  • Ganduje Na Iya Maye Gurbin Adamu A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa
  • A Karon Farko Bayan Barin Mulki, Buhari Ya Halarci Taro A Katsina

Ya ce “Babu yadda za a yi sulhu da mutumin da bai san Allah ba”.

ADVERTISEMENT

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan da ‘yan fashin daji suka kori mazauna wani kauye gaba dayansu a cikin daya daga kananan hukumomin da yake wakilta kana suka mayar da shi sansaninsu.

Dan Majalisar ya ce “Gwamnan jihar ya fito ya kalubalanci duk wani mai neman a yi sulhu da ‘yan fashin” wanda hakan ne ya kara musu karfin gwiwa a wannan tafiya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya ce akwai firgici a halin da ake ciki a jihar yanzu, domin barayin sun tsallaka titin Gurusu sun bi Barayar zaki sun tsallaka Gulbi sun je wani kauyen Rafin Gero da ake ce masa Gyado sun yi sansani, yau tsawon kwana 10 kenan.

Ya kara da cewa kalubalen da ake fuskanta a yanzu shi ne an shiga damuna, lokacin da yaki da wadannan bata-gari ke da wuya.

“Da yawan dazuka itatuwansu sun yi kore sun zama duhuwa, tsakaninka da mutane ba tazara mai yawa amma duhu ba zai barku kuga juna ba.

“Shekaran jiya sun shiga kauyukan Ruwan rana da Yashi sun kone shaguna da kuma dukiya mai yawa,” in ji Hamisu A Faru.

‘Yan fashin daji sun dauki tsawon shekaru suna kai hare-hare a jihar Zamfara da ma jihohin da suka yi makwabtaka da ita irin su; Katsina, Sakkwato da Kaduna.

Lamarin da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da sanya da dama zama ‘yan gudun hijira.

Sai dai wasu na ganin yin sulhu da ‘yan fashin dajin na iya kawo sauki ga hare-haren nasu, lamarin da ya sanya gwamnatin jihar kin amsar wannan shawara.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.