• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaba Da Musaya Zai Ingiza Kyautatuwar Aminci Tsakanin Sin Da Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
Amurka

Yayin da manyan jami’an Sin da na Amurka ke kara bunkasa musaya tsakaninsu, masharhanta na kallon hakan a matsayin hanya mafi dacewa, ta farfado da alakarsu, tare da kawar da tarnakin dake mayar da hannun agogo baya, a wannan muhimmiyar dangantaka mai tasiri ga su kansu kasashen biyu, da ma sauran sassan duniya baki daya.

A baya bayan nan, mamban hukumar siyasa, kana direktan ofishin hukumar kula da harkokin waje ta kwamitin kolin JKS, Wang Yi ya gana da sakataren wajen Amurka Antony Blinken a birnin Jakarta, a gefen taron ministocin kasashe mambobin kungiyar ASEAN, inda suka yi musaya don gane da batutuwan dake jan hankalin kasashensu. Kaza lika kafin hakan mista Blinken ya ziyarci kasar Sin a watan Yuni da ya gabata, baya ga ziyarar da sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen ta kai kasar Sin, tare da zantawa da firaministan kasar Li Qiang, da ma mataimaki sa He Lifeng a farkon watan nan na Yuli. Har ila yau, wakilin musamman na shugaban kasar Amurka game da sauyin yanayi John Kerry, shi ma ya ziyarci kasar Sin ba da jimawa ba, inda ya tattaunawa da manyan jami’an kasar game da batutuwan da suka jibanci farfado da hadin gwiwar sassan biyu kan batun sauyin yanayi.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Ko shakka babu, alakar Sin da Amurka na da matukar muhimmanci, da tasiri ga kyautatuwar rayuwar al’ummunsu, da ma na sauran kasashen duniya baki daya, kamar dai yadda jami’an sassan biyu suka sha jaddadawa.

To sai dai kuma, kamar yadda muka sha gani, akwai ’yan siyasar Amurka da dama dake siyasantar da alakar kasarsu da Sin, suna yunkurin gurbata tarihin dangantaka, da gurgunta cudanyar Amurka da Sin. Irin wadannan ’yan siyasa burinsu shi ne lahanta moriyar kasar Sin, ta hanyar shafawa kasar bakin fenti.

Lallai yunkurin irin wadannan ’yan siyasa marasa hangen nesa, na iya yin tasiri ga tunanin Amurkawa da dama, wanda hakan ka iya haifar da kyama, ko kin jinin Sin a cikin gida, matakin da ka iya yin tarnaki ga warware sabanin ra’ayi ko mahangar kasashen biyu cikin sauki. La’akari da haka, muna iya cewa, irin wadannan ’yan siyasa na haifar da babbar illa ga alakar Sin da Amurka, maimakon su zamo wakilai na gari masu kokarin dinke baraka.

LABARAI MASU NASABA

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Bisa kimar alakar Sin da Amurka, da tasirinta ga ci gaban harkokin kasa da kasa, ya dace a yi watsi da ra’ayin tsirarun ’yan siyasar Amurka, masu kokarin gurgunta tafiya mai kyau tsakanin kasashen biyu. Kuma hanyar yin hakan ita ce Amurka ta nacewa biyayya ga ka’idoji, da sanarwar hadin gwiwa uku da shugabannin kasashen biyu suka amincewa, kana Amurkan ta daina tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, kuma sassan biyu su ci gaba da tuntubar juna, bisa martaba moriyar juna, da kiyaye kimar manyan batutuwan dake jan hankalin su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba
Daga Birnin Sin

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Next Post
Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

LABARAI MASU NASABA

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.