ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaba Da Musaya Zai Ingiza Kyautatuwar Aminci Tsakanin Sin Da Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Yayin da manyan jami’an Sin da na Amurka ke kara bunkasa musaya tsakaninsu, masharhanta na kallon hakan a matsayin hanya mafi dacewa, ta farfado da alakarsu, tare da kawar da tarnakin dake mayar da hannun agogo baya, a wannan muhimmiyar dangantaka mai tasiri ga su kansu kasashen biyu, da ma sauran sassan duniya baki daya.

A baya bayan nan, mamban hukumar siyasa, kana direktan ofishin hukumar kula da harkokin waje ta kwamitin kolin JKS, Wang Yi ya gana da sakataren wajen Amurka Antony Blinken a birnin Jakarta, a gefen taron ministocin kasashe mambobin kungiyar ASEAN, inda suka yi musaya don gane da batutuwan dake jan hankalin kasashensu. Kaza lika kafin hakan mista Blinken ya ziyarci kasar Sin a watan Yuni da ya gabata, baya ga ziyarar da sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen ta kai kasar Sin, tare da zantawa da firaministan kasar Li Qiang, da ma mataimaki sa He Lifeng a farkon watan nan na Yuli. Har ila yau, wakilin musamman na shugaban kasar Amurka game da sauyin yanayi John Kerry, shi ma ya ziyarci kasar Sin ba da jimawa ba, inda ya tattaunawa da manyan jami’an kasar game da batutuwan da suka jibanci farfado da hadin gwiwar sassan biyu kan batun sauyin yanayi.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Ko shakka babu, alakar Sin da Amurka na da matukar muhimmanci, da tasiri ga kyautatuwar rayuwar al’ummunsu, da ma na sauran kasashen duniya baki daya, kamar dai yadda jami’an sassan biyu suka sha jaddadawa.

ADVERTISEMENT

To sai dai kuma, kamar yadda muka sha gani, akwai ’yan siyasar Amurka da dama dake siyasantar da alakar kasarsu da Sin, suna yunkurin gurbata tarihin dangantaka, da gurgunta cudanyar Amurka da Sin. Irin wadannan ’yan siyasa burinsu shi ne lahanta moriyar kasar Sin, ta hanyar shafawa kasar bakin fenti.

Lallai yunkurin irin wadannan ’yan siyasa marasa hangen nesa, na iya yin tasiri ga tunanin Amurkawa da dama, wanda hakan ka iya haifar da kyama, ko kin jinin Sin a cikin gida, matakin da ka iya yin tarnaki ga warware sabanin ra’ayi ko mahangar kasashen biyu cikin sauki. La’akari da haka, muna iya cewa, irin wadannan ’yan siyasa na haifar da babbar illa ga alakar Sin da Amurka, maimakon su zamo wakilai na gari masu kokarin dinke baraka.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Bisa kimar alakar Sin da Amurka, da tasirinta ga ci gaban harkokin kasa da kasa, ya dace a yi watsi da ra’ayin tsirarun ’yan siyasar Amurka, masu kokarin gurgunta tafiya mai kyau tsakanin kasashen biyu. Kuma hanyar yin hakan ita ce Amurka ta nacewa biyayya ga ka’idoji, da sanarwar hadin gwiwa uku da shugabannin kasashen biyu suka amincewa, kana Amurkan ta daina tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, kuma sassan biyu su ci gaba da tuntubar juna, bisa martaba moriyar juna, da kiyaye kimar manyan batutuwan dake jan hankalin su.

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Next Post
Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.